< Zabura 41 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
[Psalm lal David] Insewowo elos su nunku ke mwet sukasrup; Tuh LEUM GOD El ac fah kasrelos in pacl elos sun ongoiya.
2 Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
LEUM GOD El ac fah karinganulos ac liyaung moul lalos; El ac fah oru tuh elos in engan fin facl selos; El ac fah tia fuhlelosyang nu inpoun mwet lokoalok lalos.
3 Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
LEUM GOD El ac fah kasrelos in pacl in mas lalos Ac akkeyalosla.
4 Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
Nga fahk, “Nga oru ma koluk lain kom, LEUM GOD; Pakomutuk ac akkeyeyula.”
5 Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
Mwet lokoalok luk elos fahk kas upa keik. Elos kena tuh nga in misa ac in mulkinyukla.
6 Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
Elos su tuku liyeyu tia pwaye insialos; Elos porongo sramsram sutuu puspis keik Na elos som srumun yen nukewa.
7 Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
Elos su srungayu elos mahma nu sin sie sin sie keik, Elos kinauk ma na koluk ac finsrak mu in sikyak nu sik.
8 “Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
Elos fahk, “Mas in na misa se pa lal inge; El ac fah tia ku in sifil tukakek liki mwe oan kial uh.”
9 Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
Finne mwet kawuk na wowo luk, el su nga lulalfongi oemeet, Su wiyu ipeis ke mwe mongo nak, El forla likiyu.
10 Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
Pakomutuk, LEUM GOD, ac akkeyeyula, Na nga fah foloksak nu sin mwet lokoalok luk.
11 Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
Elos ac fah tia kutangyula, Ac nga fah etu lah kom insewowo sik.
12 Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
Kom ac kasreyu mweyen nga oru ma suwohs; Kom ac fah sruokyuwi yurum nwe tok.
13 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.
Kaksakin LEUM GOD, God lun Israel! Kaksakunul inge ac nu tok ma pahtpat! Amen! Amen!

< Zabura 41 >