< Zabura 41 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
Pour la fin, psaume de David. Bienheureux celui qui porte ses soins sur l’indigent et le pauvre; au jour mauvais, le Seigneur le délivrera.
2 Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
Que le Seigneur le conserve; qu’il lui donne vie et le fasse heureux sur la terre; et qu’il ne le livre point à l’âme de ses ennemis.
3 Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
Que le Seigneur lui porte secours sur le lit de sa douleur; vous avez retourné toute sa couche dans son infirmité.
4 Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
Moi j’ai dit: Seigneur, ayez pitié de moi, guérissez mon âme, parce que j’ai péché contre vous.
5 Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
Mes ennemis m’ont dit de mauvaises choses: Quand mourra-t-il, et quand périra son nom?
6 Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
Et si quelqu’un d’eux entrait pour me voir, il tenait de vains discours: son cœur s’est amassé de l’iniquité. Il sortait dehors, et il parlait
7 Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
De même. Contre moi murmuraient tous mes ennemis: contre moi ils formaient de mauvais desseins.
8 “Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
Ils ont élevé une parole inique contre moi: N’est-ce pas que celui qui dort ne se relèvera jamais?
9 Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
Car l’homme de ma paix, en qui j’ai espéré, qui mangeait mes pains, a fait éclater sur moi sa trahison.
10 Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
Mais vous, Seigneur, ayez pitié de moi et ressuscitez-moi, je leur rendrai ce qu’ils méritent.
11 Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
J’ai connu que vous m’avez aimé, en ce que mon ennemi ne se réjouira pas à mon sujet.
12 Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
Pour moi, à cause de mon innocence, vous m’avez pris sous votre protection, et vous m’avez affermi en votre présence pour toujours.
13 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.
Béni le Seigneur Dieu d’Israël, d’un siècle jusqu’à un autre siècle! Ainsi soit-il, ainsi soit-il.

< Zabura 41 >