< Zabura 41 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
Au chef de musique. Psaume de David. Bienheureux celui qui comprend le pauvre! Au mauvais jour, l’Éternel le délivrera.
2 Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
L’Éternel le gardera, et le conservera en vie: il sera rendu heureux sur la terre, et tu ne le livreras point à l’animosité de ses ennemis.
3 Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
L’Éternel le soutiendra sur un lit de langueur. Tu transformeras tout son lit, quand il sera malade.
4 Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
J’ai dit: Éternel! use de grâce envers moi, guéris mon âme, car j’ai péché contre toi.
5 Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
Mes ennemis me souhaitent du mal: Quand mourra-t-il? Quand périra son nom?
6 Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
Et si l’un vient me voir, il dit des paroles de fausseté; son cœur amasse par-devers lui l’iniquité; … il sort dehors, il en parle.
7 Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
Tous ceux qui me haïssent chuchotent ensemble contre moi; ils imaginent du mal contre moi:
8 “Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
Quelque œuvre de Bélial est attachée à lui, et maintenant qu’il est couché, il ne se relèvera plus.
9 Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
Mon intime ami aussi, en qui je me confiais, qui mangeait mon pain, a levé le talon contre moi.
10 Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
Et toi, Éternel! use de grâce envers moi et relève-moi, et je [le] leur rendrai.
11 Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
À ceci je connais que tu prends plaisir en moi, c’est que mon ennemi ne triomphe pas de moi.
12 Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
Et moi, tu m’as maintenu dans mon intégrité, et tu m’as établi devant toi pour toujours.
13 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.
Béni soit l’Éternel, le Dieu d’Israël, de l’éternité jusqu’en éternité! Amen, oui, amen!

< Zabura 41 >