< Zabura 41 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
For the Chief Musician. A Psalm of David. Blessed is he that considereth the poor: the LORD will deliver him in the day of evil.
2 Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
The LORD will preserve him, and keep him alive, and he shall be blessed upon the earth; and deliver not thou him unto the will of his enemies.
3 Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
The LORD will support him upon the couch of languishing: thou makest all his bed in his sickness.
4 Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
I said, O LORD, have mercy upon me: heal my soul; for I have sinned against thee.
5 Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
Mine enemies speak evil against me, [saying], When shall he die, and his name perish?
6 Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
And if he come to see [me], he speaketh vanity; his heart gathereth iniquity to itself: when he goeth abroad, he telleth it.
7 Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
All that hate me whisper together against me: against me do they devise my hurt.
8 “Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
An evil disease, [say they], cleaveth fast unto him: and now that he lieth he shall rise up no more.
9 Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
Yea, mine own familiar friend, in whom I trusted, which did eat of my bread, hath lifted up his heel against me.
10 Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
But thou, O LORD, have mercy upon me, and raise me up, that I may requite them.
11 Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
By this I know that thou delightest in me, because mine enemy doth not triumph over me.
12 Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
And as for me, thou upholdest me in mine integrity, and settest me before thy face for ever.
13 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.
Blessed be the LORD, the God of Israel, from everlasting and to everlasting. Amen, and Amen.