< Zabura 41 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
For the leader; for Jeduthun. A psalm of David. Happy are those who consider the weak; in the day of misfortune the Lord will deliver them.
2 Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
He will keep them safe, happy, and long in the land, and not give them up to the rage of their foes.
3 Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
The Lord will sustain them on bed of languishing; tending their sickness, as long as they lie.
4 Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
For this cause I say, “Lord, show me your favor; heal me, because I have sinned against you.”
5 Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
My enemies speak of me nothing but evil, “When will he die, and his name pass away?”
6 Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
When one comes to see me, their words ring hollow; their heart keeps gathering mischief the while; and when they go out, they give it speech.
7 Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
In secret they whisper together against me, all those who hate me plot evil against me.
8 “Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
“Some fatal disease has fastened upon him; and now that he lies, he will rise up no more.”
9 Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
My most trusted friend, on whom I relied, who ate of my bread, has turned against me.
10 Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
But do you, Lord, graciously raise me up, that I may pay them their due reward.
11 Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
By this will I know you delight in me: if my foes may not shout over me in triumph.
12 Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
For my innocence you uphold me, and set me forever before your face.
13 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.
Blessed be the Lord, the God of Israel, from everlasting to everlasting, Amen and Amen.