< Zabura 41 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
Blessed is he that considers the poor: the LORD will deliver him in time of trouble.
2 Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
The LORD will preserve him, and keep him alive; and he shall be blessed on the earth: and you will not deliver him to the will of his enemies.
3 Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
The LORD will strengthen him on the bed of languishing: you will make all his bed in his sickness.
4 Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
I said, LORD, be merciful to me: heal my soul; for I have sinned against you.
5 Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
My enemies speak evil of me, When shall he die, and his name perish?
6 Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
And if he come to see me, he speaks vanity: his heart gathers iniquity to itself; when he goes abroad, he tells it.
7 Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
All that hate me whisper together against me: against me do they devise my hurt.
8 “Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
An evil disease, say they, sticks fast to him: and now that he lies he shall rise up no more.
9 Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
Yes, my own familiar friend, in whom I trusted, which did eat of my bread, has lifted up his heel against me.
10 Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
But you, O LORD, be merciful to me, and raise me up, that I may requite them.
11 Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
By this I know that you favor me, because my enemy does not triumph over me.
12 Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
And as for me, you uphold me in my integrity, and set me before your face for ever.
13 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.
Blessed be the LORD God of Israel from everlasting, and to everlasting. Amen, and Amen.

< Zabura 41 >