< Zabura 41 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
For the end, a Psalm of David. Blessed [is the man] who thinks, on the poor and needy: the Lord shall deliver him in an evil day.
2 Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
May the Lord preserve him and keep him alive, and bless him on the earth, and not deliver him into the hands of his enemy.
3 Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
May the Lord help him upon the bed of his pain; you have made all his bed in his sickness.
4 Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
I said, O Lord, have mercy upon me; heal my soul; for I have sinned against you.
5 Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
Mine enemies have spoken evil against me, [saying], When shall he die, and his name perish?
6 Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
And if he came to see [me], his heart spoke vainly; he gathered iniquity to himself; he went forth and spoke in like manner.
7 Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
All my enemies whispered against me; against me they devised my hurt.
8 “Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
They denounced a wicked word against me, [saying], Now that he lies, shall he not rise up again?
9 Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
For even the man of my peace, in whom I trusted, who ate my bread, lifted up [his] heel against me.
10 Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
But you, O Lord, have compassion upon me, and raise me up, and I shall requite them.
11 Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
By this I know that you have delighted in me, because mine enemy shall not rejoice over me.
12 Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
But you did help me because of [mine] innocence, and have established me before you for ever.
13 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.
Blessed [be] the Lord God of Israel from everlasting, and to everlasting. So be it, so be it.

< Zabura 41 >