< Zabura 41 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
Blessed is he who considers a poor man. Jehovah will deliver him in the day of evil.
2 Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
Jehovah will preserve him, and keep him alive, and he shall be blessed upon the earth. And thou do not deliver him to the will of his enemies.
3 Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
Jehovah will support him upon the bed of languishing. Thou will make all his bed in his sickness.
4 Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
I said, O Jehovah, have mercy upon me. Heal my soul, for I have sinned against thee.
5 Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
My enemies speak evil against me, saying, When will he die, and his name perish?
6 Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
And if he comes to see me, he speaks falsehood. His heart gathers iniquity to itself. When he goes abroad, he tells it.
7 Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
All who hate me whisper together against me. Against me they devise my hurt.
8 “Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
An evil disease, they say, clings firm to him. And now that he lies he shall rise up no more.
9 Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
Yea, my own familiar friend, in whom I trusted, who ate of my bread, has lifted up his heel against me.
10 Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
But thou, O Jehovah, have mercy upon me, and raise me up that I may requite them.
11 Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
By this I know that thou delight in me, because my enemy does not triumph over me.
12 Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
And as for me, thou uphold me in my integrity, and set me before thy face forever.
13 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.
Blessed be Jehovah, the God of Israel, from everlasting and to everlasting. Truly, and Truly.