< Zabura 40 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Na jira da haƙuri ga Ubangiji; ya juya wurina ya kuma ji kukata.
В конец, псалом Давиду. Терпя потерпех Господа, и внят ми и услыша молитву мою:
2 Ya ɗaga ni daga rami marar fāɗi, daga laka da taɓo; ya sa ƙafafuna a kan dutse ya kuma ba ni tsayayyen wuri don in tsaya.
и возведе мя от рова страстей и от брения тины, и постави на камени нозе мои и исправи стопы моя:
3 Ya sa sabuwar waƙa a bakina, waƙar yabo ga Allahna. Da yawa za su gani su tsorata su kuma dogara ga Ubangiji.
и вложи во уста моя песнь нову, пение Богу нашему. Узрят мнози и убоятся, и уповают на Господа.
4 Mai albarka ne mutumin da ya mai da Ubangiji abin dogararsa, wanda ba ya kula da masu girman kai, waɗanda suka juya ga allolin ƙarya.
Блажен муж, емуже есть имя Господне упование его, и не призре в суеты и неистовления ложная.
5 Da yawa ne, ya Ubangiji Allahna, abubuwan banmamakin da ka aikata. Abubuwan da ka shirya mana. Ba wanda zai iya faɗa maka su; a ce zan yi magana in faɗe su, za su wuce gaban misali a furta.
Многа сотворил еси Ты, Господи Боже мой, чудеса Твоя, и помышлением Твоим несть кто уподобится Тебе: возвестих и глаголах: умножишася паче числа.
6 Hadaya da sadaka ba ka sha’awa, amma kunnuwana ka huda; hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka bukata.
Жертвы и приношения не восхотел еси, тело же свершил ми еси: всесожжений и о гресе не взыскал еси.
7 Sa’an nan na ce, “Ga ni, na zo, kamar yadda yake a rubuce game da ni cikin littafi.
Тогда рех: се, прииду: в главизне книжне писано есть о мне:
8 Ina sha’awar aikata nufinka, ya Allahna; dokar tana cikin zuciyata.”
еже сотворити волю Твою, Боже мой, восхотех, и закон Твой посреде чрева моего.
9 Na yi shelar adalcinka cikin babban taro; ba na rufe leɓunana, kamar yadda ka sani, ya Ubangiji.
Благовестих правду в церкви велицей, се, устнам моим не возбраню: Господи, Ты разумел еси.
10 Ba na ɓoye adalcinka cikin zuciyata; ina maganar amincinka da cetonka. Ban ɓoye ƙaunarka da gaskiyarka a gaban taron jama’arka mai girma ba.
Правду Твою не скрых в сердцы моем, истину Твою и спасение Твое рех, не скрых милость Твою и истину Твою от сонма многа.
11 Kada ka hana mini jinƙanka, ya Ubangiji; bari ƙaunarka da gaskiyarka kullum su kāre ni.
Ты же, Господи, не удали щедрот Твоих от мене: милость Твоя и истина Твоя выну да заступите мя.
12 Gama damuwoyin da suka wuce misali sun kewaye ni; zunubaina sun mamaye ni, kuma ba na iya gani. Sun fi gashin kaina yawa, har ma na fid da zuciya.
Яко одержаша мя злая, имже несть числа: постигоша мя беззакония моя, и не возмогох зрети: умножишася паче влас главы моея, и сердце мое остави мя.
13 Ka ji daɗin cetona, ya Ubangiji; Ya Ubangiji, ka zo da sauri ka taimake ni.
Благоволи, Господи, избавити мя: Господи, во еже помощи ми, вонми.
14 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan waɗanda suke neman lalacewata su koma baya da kunya.
Да постыдятся и посрамятся вкупе ищущии душу мою, изяти ю: да возвратятся вспять и постыдятся хотящии ми злая.
15 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su sha mamaki saboda kunyar da za su sha.
Да приимут абие студ свой глаголющии ми: благоже, благоже.
16 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Ubangiji mai girma ne!”
Да возрадуются и возвеселятся о Тебе вси ищущии Тебе, Господи, и да рекут выну, да возвеличится Господь, любящии спасение Твое.
17 Ni dai matalauci ne da mai bukata; bari Ubangiji yă tuna da ni. Kai ne taimakona da mai cetona; Ya Allahna, kada ka jinkirta.
Аз же нищь есмь и убог, Господь попечется о мне: помощник мой и защититель мой еси ты, Боже мой, не закосни.

< Zabura 40 >