< Zabura 40 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Na jira da haƙuri ga Ubangiji; ya juya wurina ya kuma ji kukata.
Kumqondisi wokuhlabela. ElikaDavida. Ihubo. Ngamlindela ngesineke uThixo; waphendukela ngakimi wezwa ukukhala kwami.
2 Ya ɗaga ni daga rami marar fāɗi, daga laka da taɓo; ya sa ƙafafuna a kan dutse ya kuma ba ni tsayayyen wuri don in tsaya.
Wangenyula emgodini otshonayo, wangikhupha edakeni lexhaphozini; wamisa inyawo zami edwaleni, wangipha indawo eqinileyo yokuma.
3 Ya sa sabuwar waƙa a bakina, waƙar yabo ga Allahna. Da yawa za su gani su tsorata su kuma dogara ga Ubangiji.
Wangipha ingoma entsha emlonyeni wami, ihubo lokudumisa kuNkulunkulu wethu. Abanengi bazabona besabe babeke ithemba labo kuThixo.
4 Mai albarka ne mutumin da ya mai da Ubangiji abin dogararsa, wanda ba ya kula da masu girman kai, waɗanda suka juya ga allolin ƙarya.
Ubusisiwe umuntu owenza uThixo abe lithemba lakhe, ongathembi abazigqajayo, lalabo abaqambukela kubonkulunkulu bamanga.
5 Da yawa ne, ya Ubangiji Allahna, abubuwan banmamakin da ka aikata. Abubuwan da ka shirya mana. Ba wanda zai iya faɗa maka su; a ce zan yi magana in faɗe su, za su wuce gaban misali a furta.
Zinengi, Thixo, Nkulunkulu wami, izimangaliso ozenzileyo. Izinto owasilungiselela zona kakho ongazibala kuwe; aluba bengingakhuluma loba ngilandise ngazo, zingaba zinengi ngokweqileyo ukuzibalisa.
6 Hadaya da sadaka ba ka sha’awa, amma kunnuwana ka huda; hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka bukata.
Kawufisanga imihlatshelo leminikelo kodwa indlebe zami uzikleklile; iminikelo yokutshiswa leminikelo yesono kawuzange uyidinge.
7 Sa’an nan na ce, “Ga ni, na zo, kamar yadda yake a rubuce game da ni cikin littafi.
Lapho-ke ngasengisithi, “Ngilapha, sengifikile kulotshiwe ngami emqulwini.
8 Ina sha’awar aikata nufinka, ya Allahna; dokar tana cikin zuciyata.”
Ngiyakunxwanela ukwenza intando yakho, Oh Nkulunkulu wami; umthetho wakho usenhliziyweni yami.”
9 Na yi shelar adalcinka cikin babban taro; ba na rufe leɓunana, kamar yadda ka sani, ya Ubangiji.
Ngiyafakaza ngokulunga ngisemhlanganweni omkhulu; angizivali izindebe zami, njengoba usazi, Oh Thixo.
10 Ba na ɓoye adalcinka cikin zuciyata; ina maganar amincinka da cetonka. Ban ɓoye ƙaunarka da gaskiyarka a gaban taron jama’arka mai girma ba.
Ukulunga kwakho kangikufihli enhliziyweni yami; ngikhuluma ngokuthembeka kwakho lokusindisa kwakho. Kangilufihli uthando lwakho leqiniso lakho emhlanganweni omkhulu.
11 Kada ka hana mini jinƙanka, ya Ubangiji; bari ƙaunarka da gaskiyarka kullum su kāre ni.
Ungasigodli isihawu sakho kimi, Oh Thixo; sengathi uthando lwakho leqiniso lakho kungahlala kungivikela.
12 Gama damuwoyin da suka wuce misali sun kewaye ni; zunubaina sun mamaye ni, kuma ba na iya gani. Sun fi gashin kaina yawa, har ma na fid da zuciya.
Phela inhlupheko ezingelakubalwa zingihanqile; izono zami sezingificile, kangisaboni. Zinengi kulenwele zekhanda lami, njalo inhliziyo yami isiphela amandla.
13 Ka ji daɗin cetona, ya Ubangiji; Ya Ubangiji, ka zo da sauri ka taimake ni.
Jabula, awu Thixo, ungisindise; awu Thixo, woza masinyane uzongisiza.
14 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan waɗanda suke neman lalacewata su koma baya da kunya.
Sengathi bonke abafuna ukuqeda impilo yami bangayangiswa basanganiswe; sengathi bonke abafisa ukungidiliza bangabuyiselwa emuva beyangekile.
15 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su sha mamaki saboda kunyar da za su sha.
Sengathi bonke abathi kimi, “Ehe, Ehe!” banganengwa lihlazo labo.
16 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Ubangiji mai girma ne!”
Kodwa akuthi bonke abakudingayo bathokoze bajabule kuwe; akuthi labo abathanda insindiso yakho bahlale besithi, “UThixo kadunyiswe!”
17 Ni dai matalauci ne da mai bukata; bari Ubangiji yă tuna da ni. Kai ne taimakona da mai cetona; Ya Allahna, kada ka jinkirta.
Kodwa mina ngiyahlupheka, ngiyaswela; sengathi iNkosi ingangikhumbula. Ilusizo lwami lomkhululi wami; Oh Nkulunkulu wami, ungalibali.