< Zabura 40 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Na jira da haƙuri ga Ubangiji; ya juya wurina ya kuma ji kukata.
Au maître-chantre. — Psaume de David. J'ai fermement attendu l'Éternel; Il s'est incliné vers moi, il a entendu mes cris.
2 Ya ɗaga ni daga rami marar fāɗi, daga laka da taɓo; ya sa ƙafafuna a kan dutse ya kuma ba ni tsayayyen wuri don in tsaya.
Il m'a fait remonter de la fosse de destruction. Du bourbier fangeux. Il a posé mes pieds sur le roc, Il a affermi mes pas.
3 Ya sa sabuwar waƙa a bakina, waƙar yabo ga Allahna. Da yawa za su gani su tsorata su kuma dogara ga Ubangiji.
Il a mis dans ma bouche un chant nouveau, Un hymne à la louange de notre Dieu. Bien des hommes, témoins de ces délivrances. Craindront l'Éternel et se confieront en lui.
4 Mai albarka ne mutumin da ya mai da Ubangiji abin dogararsa, wanda ba ya kula da masu girman kai, waɗanda suka juya ga allolin ƙarya.
Heureux l'homme qui place en l'Éternel sa confiance, Qui ne se tourne pas vers les orgueilleux Et vers ceux que le mensonge égare!
5 Da yawa ne, ya Ubangiji Allahna, abubuwan banmamakin da ka aikata. Abubuwan da ka shirya mana. Ba wanda zai iya faɗa maka su; a ce zan yi magana in faɗe su, za su wuce gaban misali a furta.
Éternel, mon Dieu, tu as multiplié Tes merveilles et tes dispensations en notre faveur: Impossible d'en faire le compte devant toi! Je voudrais les proclamer et les publier: Elles sont trop nombreuses pour que je puisse les énumérer.
6 Hadaya da sadaka ba ka sha’awa, amma kunnuwana ka huda; hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka bukata.
Tu ne prends plaisir ni aux sacrifices ni aux offrandes; Mais tu m'as donné des oreilles attentives: Tu ne demandes pas d'holocauste, ni de sacrifice pour le péché.
7 Sa’an nan na ce, “Ga ni, na zo, kamar yadda yake a rubuce game da ni cikin littafi.
Alors j'ai dit: «Me voici, je viens. Avec le rouleau du livre qui est écrit pour moi.»
8 Ina sha’awar aikata nufinka, ya Allahna; dokar tana cikin zuciyata.”
Mon Dieu, je prends plaisir à faire ta volonté. Et ta loi est au fond de mon coeur.
9 Na yi shelar adalcinka cikin babban taro; ba na rufe leɓunana, kamar yadda ka sani, ya Ubangiji.
J'annonce ta justice devant la foule assemblée. Je ne tiens pas mes lèvres fermées, Tu le sais, ô Éternel!
10 Ba na ɓoye adalcinka cikin zuciyata; ina maganar amincinka da cetonka. Ban ɓoye ƙaunarka da gaskiyarka a gaban taron jama’arka mai girma ba.
Je ne fais pas de ta justice un secret caché dans mon coeur; Je proclame ta fidélité et tes délivrances; Je ne tais point ta bonté ni ta vérité. Devant la foule assemblée.
11 Kada ka hana mini jinƙanka, ya Ubangiji; bari ƙaunarka da gaskiyarka kullum su kāre ni.
Toi donc, ô Éternel, ne me refuse pas ta miséricorde! Que ta bonté et ta fidélité veillent constamment sur moi!
12 Gama damuwoyin da suka wuce misali sun kewaye ni; zunubaina sun mamaye ni, kuma ba na iya gani. Sun fi gashin kaina yawa, har ma na fid da zuciya.
Car des maux sans nombre m'environnent. Mes iniquités m'accablent; Ma vue en est obscurcie; Elles surpassent en nombre les cheveux de ma tête, Et mon coeur défaille.
13 Ka ji daɗin cetona, ya Ubangiji; Ya Ubangiji, ka zo da sauri ka taimake ni.
Éternel, daigne me délivrer! Éternel, accours à mon aide!
14 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan waɗanda suke neman lalacewata su koma baya da kunya.
Qu'ils soient confus et qu'ils rougissent Tous ceux qui cherchent à m'ôter la vie! Qu'ils reculent et soient couverts de honte Tous ceux qui prennent plaisir à ma perte!
15 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su sha mamaki saboda kunyar da za su sha.
Que leur ignominie les fasse frémir d'épouvante. Ceux qui disent de moi: «Ah! Ah!»
16 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Ubangiji mai girma ne!”
Que tous ceux qui te recherchent S'égaient et se réjouissent en toi! Que ceux qui espèrent en ton secours Disent sans cesse: «Gloire soit à l'Éternel!»
17 Ni dai matalauci ne da mai bukata; bari Ubangiji yă tuna da ni. Kai ne taimakona da mai cetona; Ya Allahna, kada ka jinkirta.
Je suis affligé et misérable; Le Seigneur aura soin de moi. Tu es mon aide et mon libérateur: mon Dieu, ne tarde pas!

< Zabura 40 >