< Zabura 40 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Na jira da haƙuri ga Ubangiji; ya juya wurina ya kuma ji kukata.
Au maître chantre. Cantique de David. J'attendis fermement l'Éternel; et se penchant vers moi, Il écouta ma plainte.
2 Ya ɗaga ni daga rami marar fāɗi, daga laka da taɓo; ya sa ƙafafuna a kan dutse ya kuma ba ni tsayayyen wuri don in tsaya.
Et Il me retira de l'horreur de la fosse, de la fange du bourbier; et Il fit poser mon pied sur le roc, affermissant mes pas;
3 Ya sa sabuwar waƙa a bakina, waƙar yabo ga Allahna. Da yawa za su gani su tsorata su kuma dogara ga Ubangiji.
et Il mit dans ma bouche un cantique nouveau, les louanges de notre Dieu. Témoins de ces choses, plusieurs craindront, et auront confiance dans l'Éternel.
4 Mai albarka ne mutumin da ya mai da Ubangiji abin dogararsa, wanda ba ya kula da masu girman kai, waɗanda suka juya ga allolin ƙarya.
Heureux l'homme qui choisit l'Éternel pour placer en lui sa confiance, et ne s'adresse pas aux présomptueux, aux menteurs!
5 Da yawa ne, ya Ubangiji Allahna, abubuwan banmamakin da ka aikata. Abubuwan da ka shirya mana. Ba wanda zai iya faɗa maka su; a ce zan yi magana in faɗe su, za su wuce gaban misali a furta.
Il est grand, Éternel, mon Dieu, le nombre des miracles et des décrets que tu fis pour nous; rien n'est comparable à toi: je voudrais les raconter et les dire, il y en a trop pour les énumérer.
6 Hadaya da sadaka ba ka sha’awa, amma kunnuwana ka huda; hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka bukata.
Ce n'est ni la victime, ni l'offrande que tu aimes, (tu as ouvert mes oreilles à cette instruction) l'holocauste et l'expiation, ce n'est pas ce que tu demandes.
7 Sa’an nan na ce, “Ga ni, na zo, kamar yadda yake a rubuce game da ni cikin littafi.
Aussi j'ai dit: « Voici, je viens; c'est ce que me prescrit le livre de la loi.
8 Ina sha’awar aikata nufinka, ya Allahna; dokar tana cikin zuciyata.”
Faire ta volonté, mon Dieu, c'est mon désir, et ta loi est dans mon cœur. »
9 Na yi shelar adalcinka cikin babban taro; ba na rufe leɓunana, kamar yadda ka sani, ya Ubangiji.
Je proclame [ta] justice dans la grande assemblée; voici, je ne tiens point mes lèvres fermées: Éternel, tu le sais!
10 Ba na ɓoye adalcinka cikin zuciyata; ina maganar amincinka da cetonka. Ban ɓoye ƙaunarka da gaskiyarka a gaban taron jama’arka mai girma ba.
Je ne cèle point ta justice au dedans de mon cœur; je dis ta fidélité et ton secours, je ne dissimule point ta grâce et ta fidélité à la grande assemblée.
11 Kada ka hana mini jinƙanka, ya Ubangiji; bari ƙaunarka da gaskiyarka kullum su kāre ni.
Et toi, Éternel, ne retiens pas non plus ta miséricorde envers moi! Que ta grâce et ta fidélité me gardent toujours!
12 Gama damuwoyin da suka wuce misali sun kewaye ni; zunubaina sun mamaye ni, kuma ba na iya gani. Sun fi gashin kaina yawa, har ma na fid da zuciya.
Car je suis entouré de maux sans nombre; de mes péchés je reçois des atteintes, je ne puis les voir, ils sont plus nombreux que les cheveux de ma tête, et mon cœur m'abandonne.
13 Ka ji daɗin cetona, ya Ubangiji; Ya Ubangiji, ka zo da sauri ka taimake ni.
O Éternel, daigne me sauver! Éternel, accours à mon aide!
14 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan waɗanda suke neman lalacewata su koma baya da kunya.
Qu'ils soient tous ensemble couverts de honte et d'affronts ceux qui attentent à ma vie, pour me la ravir! Qu'ils reculent confondus ceux qui veulent mon malheur!
15 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su sha mamaki saboda kunyar da za su sha.
Qu'ils soient stupéfaits de leur propre ignominie ceux qui disent: Le voilà! Le voilà!
16 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Ubangiji mai girma ne!”
Ainsi tu feras le ravissement et la joie de tous ceux qui te cherchent; ils diront sans cesse: « Grand est l'Éternel! » ceux qui désirent ton secours.
17 Ni dai matalauci ne da mai bukata; bari Ubangiji yă tuna da ni. Kai ne taimakona da mai cetona; Ya Allahna, kada ka jinkirta.
Je suis un pauvre et un indigent, mais le Seigneur pense à moi. Tu es mon aide et mon libérateur! Mon Dieu, ne tarde pas!