< Zabura 40 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Na jira da haƙuri ga Ubangiji; ya juya wurina ya kuma ji kukata.
Psaume de David, [donné] au maître chantre. J'ai attendu patiemment l'Eternel, et il s'est tourné vers moi, et a ouï mon cri.
2 Ya ɗaga ni daga rami marar fāɗi, daga laka da taɓo; ya sa ƙafafuna a kan dutse ya kuma ba ni tsayayyen wuri don in tsaya.
Il m'a fait remonter hors d'un puits bruyant, et d'un bourbier fangeux; il a mis mes pieds sur un roc, [et] a assuré mes pas.
3 Ya sa sabuwar waƙa a bakina, waƙar yabo ga Allahna. Da yawa za su gani su tsorata su kuma dogara ga Ubangiji.
Et il a mis en ma bouche un nouveau Cantique, qui est la louange de notre Dieu. Plusieurs verront cela, et ils craindront, et se confieront en l'Eternel.
4 Mai albarka ne mutumin da ya mai da Ubangiji abin dogararsa, wanda ba ya kula da masu girman kai, waɗanda suka juya ga allolin ƙarya.
Ô que bienheureux est l'homme qui s'est proposé l'Eternel pour son assurance, et qui ne regarde point aux orgueilleux, ni à ceux qui se détournent vers le mensonge!
5 Da yawa ne, ya Ubangiji Allahna, abubuwan banmamakin da ka aikata. Abubuwan da ka shirya mana. Ba wanda zai iya faɗa maka su; a ce zan yi magana in faɗe su, za su wuce gaban misali a furta.
Eternel mon Dieu! tu as fait que tes merveilles et tes pensées envers nous sont en grand nombre; Il n'est pas possible de les arranger devant toi: les veux-je réciter et dire? elles sont en si grand nombre, que je ne les saurais raconter.
6 Hadaya da sadaka ba ka sha’awa, amma kunnuwana ka huda; hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka bukata.
Tu ne prends point plaisir au sacrifice ni au gâteau; [mais] tu m'as percé les oreilles; tu n'as point demandé d'holocauste, ni d'oblation pour le péché.
7 Sa’an nan na ce, “Ga ni, na zo, kamar yadda yake a rubuce game da ni cikin littafi.
Alors j'ai dit: Voici, je viens, il est écrit de moi au rôle du Livre;
8 Ina sha’awar aikata nufinka, ya Allahna; dokar tana cikin zuciyata.”
Mon Dieu, j'ai pris plaisir à faire ta volonté, et ta Loi est au-dedans de mes entrailles.
9 Na yi shelar adalcinka cikin babban taro; ba na rufe leɓunana, kamar yadda ka sani, ya Ubangiji.
J'ai prêché ta justice dans la grande assemblée; voilà, je n'ai point retenu mes lèvres; tu le sais, ô Eternel!
10 Ba na ɓoye adalcinka cikin zuciyata; ina maganar amincinka da cetonka. Ban ɓoye ƙaunarka da gaskiyarka a gaban taron jama’arka mai girma ba.
Je n'ai point caché ta justice, [qui est] au-dedans de mon cœur; j'ai déclaré ta fidélité et ta délivrance; je n'ai point scellé ta gratuité ni ta vérité dans la grande assemblée.
11 Kada ka hana mini jinƙanka, ya Ubangiji; bari ƙaunarka da gaskiyarka kullum su kāre ni.
[Et] toi, Eternel! ne m'épargne point tes compassions; que ta gratuité et ta vérité me gardent continuellement.
12 Gama damuwoyin da suka wuce misali sun kewaye ni; zunubaina sun mamaye ni, kuma ba na iya gani. Sun fi gashin kaina yawa, har ma na fid da zuciya.
Car des maux sans nombre m'ont environné; mes iniquités m'ont atteint, et je ne les ai pu voir; elles surpassent en nombre les cheveux de ma tête, et mon cœur m'a abandonné.
13 Ka ji daɗin cetona, ya Ubangiji; Ya Ubangiji, ka zo da sauri ka taimake ni.
Eternel, veuille me délivrer; Eternel, hâte-toi de venir à mon secours.
14 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan waɗanda suke neman lalacewata su koma baya da kunya.
Que ceux-là soient tous honteux et rougissent ensemble qui cherchent mon âme pour la perdre; et que ceux qui prennent plaisir à mon malheur, retournent en arrière, et soient confus.
15 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su sha mamaki saboda kunyar da za su sha.
Que ceux qui disent de moi: Aha! Aha! soient consumés, en récompense de la honte qu'ils m'ont faite.
16 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Ubangiji mai girma ne!”
Que tous ceux qui te cherchent, s'égayent et se réjouissent en toi; [et] que ceux qui aiment ta délivrance, disent continuellement: Magnifié soit l'Eternel.
17 Ni dai matalauci ne da mai bukata; bari Ubangiji yă tuna da ni. Kai ne taimakona da mai cetona; Ya Allahna, kada ka jinkirta.
Or je suis affligé et misérable, [mais] le Seigneur a soin de moi; tu es mon secours et mon libérateur; mon Dieu ne tarde point.

< Zabura 40 >