< Zabura 40 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Na jira da haƙuri ga Ubangiji; ya juya wurina ya kuma ji kukata.
Pour le chef musicien. Un psaume de David. J'ai attendu patiemment l'Éternel. Il s'est tourné vers moi, et a entendu mon cri.
2 Ya ɗaga ni daga rami marar fāɗi, daga laka da taɓo; ya sa ƙafafuna a kan dutse ya kuma ba ni tsayayyen wuri don in tsaya.
Il m'a aussi fait sortir d'une horrible fosse, de l'argile glaiseuse. Il a posé mes pieds sur un rocher, et m'a donné un endroit ferme où me tenir.
3 Ya sa sabuwar waƙa a bakina, waƙar yabo ga Allahna. Da yawa za su gani su tsorata su kuma dogara ga Ubangiji.
Il a mis dans ma bouche un chant nouveau, la louange à notre Dieu. Beaucoup le verront, auront peur et se confieront à Yahvé.
4 Mai albarka ne mutumin da ya mai da Ubangiji abin dogararsa, wanda ba ya kula da masu girman kai, waɗanda suka juya ga allolin ƙarya.
Heureux l'homme qui fait confiance à Yahvé! et ne respecte pas les orgueilleux, ni ceux qui se détournent vers le mensonge.
5 Da yawa ne, ya Ubangiji Allahna, abubuwan banmamakin da ka aikata. Abubuwan da ka shirya mana. Ba wanda zai iya faɗa maka su; a ce zan yi magana in faɗe su, za su wuce gaban misali a furta.
Nombreuses sont, Yahvé, mon Dieu, les merveilles que tu as faites, et vos pensées qui sont envers nous. Ils ne peuvent pas être déclarés à votre place. Si je devais les déclarer et en parler, ils sont plus nombreux qu'on ne peut les compter.
6 Hadaya da sadaka ba ka sha’awa, amma kunnuwana ka huda; hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka bukata.
Sacrifice et offrande que tu ne désirais pas. Vous m'avez ouvert les oreilles. Tu n'as pas exigé l'holocauste et le sacrifice pour le péché.
7 Sa’an nan na ce, “Ga ni, na zo, kamar yadda yake a rubuce game da ni cikin littafi.
Alors je dis: « Voici, je suis venu. Il est écrit sur moi dans le livre du rouleau.
8 Ina sha’awar aikata nufinka, ya Allahna; dokar tana cikin zuciyata.”
Je prends plaisir à faire ta volonté, mon Dieu. Oui, ta loi est dans mon cœur. »
9 Na yi shelar adalcinka cikin babban taro; ba na rufe leɓunana, kamar yadda ka sani, ya Ubangiji.
J'ai annoncé la bonne nouvelle de la justice dans la grande assemblée. Voici, je ne scellerai pas mes lèvres, Yahvé, tu le sais.
10 Ba na ɓoye adalcinka cikin zuciyata; ina maganar amincinka da cetonka. Ban ɓoye ƙaunarka da gaskiyarka a gaban taron jama’arka mai girma ba.
Je n'ai pas caché ta justice dans mon cœur. J'ai déclaré ta fidélité et ton salut. Je n'ai pas caché ta bonté et ta vérité à la grande assemblée.
11 Kada ka hana mini jinƙanka, ya Ubangiji; bari ƙaunarka da gaskiyarka kullum su kāre ni.
Ne me cache pas ta miséricorde, Yahvé. Que ta bonté et ta vérité me préservent continuellement.
12 Gama damuwoyin da suka wuce misali sun kewaye ni; zunubaina sun mamaye ni, kuma ba na iya gani. Sun fi gashin kaina yawa, har ma na fid da zuciya.
Car d'innombrables maux m'ont entouré. Mes iniquités m'ont rattrapé, si bien que je ne suis pas capable de lever les yeux. Ils sont plus nombreux que les cheveux de ma tête. Mon cœur m'a lâché.
13 Ka ji daɗin cetona, ya Ubangiji; Ya Ubangiji, ka zo da sauri ka taimake ni.
Sois heureux, Yahvé, de me délivrer. Dépêche-toi de m'aider, Yahvé.
14 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan waɗanda suke neman lalacewata su koma baya da kunya.
Qu'ils soient déçus et confondus ensemble, ceux qui cherchent mon âme pour la détruire. Qu'on fasse reculer et qu'on déshonore ceux qui se plaisent à me faire du mal.
15 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su sha mamaki saboda kunyar da za su sha.
Qu'ils soient désolés à cause de leur honte, ceux qui me disent: « Aha! Aha! »
16 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Ubangiji mai girma ne!”
Que tous ceux qui te cherchent se réjouissent et se réjouissent en toi. Que ceux qui aiment votre salut disent sans cesse: « Que Yahvé soit exalté! »
17 Ni dai matalauci ne da mai bukata; bari Ubangiji yă tuna da ni. Kai ne taimakona da mai cetona; Ya Allahna, kada ka jinkirta.
Mais moi, je suis pauvre et indigent. Que le Seigneur pense à moi. Tu es mon aide et mon libérateur. Ne tardez pas, mon Dieu.