< Zabura 40 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Na jira da haƙuri ga Ubangiji; ya juya wurina ya kuma ji kukata.
For the chief musician. A psalm of David. I waited patiently for Yahweh; he listened to me and heard my cry.
2 Ya ɗaga ni daga rami marar fāɗi, daga laka da taɓo; ya sa ƙafafuna a kan dutse ya kuma ba ni tsayayyen wuri don in tsaya.
He brought me up out of a horrible pit, out of the miry clay, and he set my feet on a rock and made my steps secure.
3 Ya sa sabuwar waƙa a bakina, waƙar yabo ga Allahna. Da yawa za su gani su tsorata su kuma dogara ga Ubangiji.
He has put a new song in my mouth, praise to our God. Many will see it and honor him and will trust in Yahweh.
4 Mai albarka ne mutumin da ya mai da Ubangiji abin dogararsa, wanda ba ya kula da masu girman kai, waɗanda suka juya ga allolin ƙarya.
Blessed is the man who makes Yahweh his trust and does not honor the proud or those who turn away from him to lies.
5 Da yawa ne, ya Ubangiji Allahna, abubuwan banmamakin da ka aikata. Abubuwan da ka shirya mana. Ba wanda zai iya faɗa maka su; a ce zan yi magana in faɗe su, za su wuce gaban misali a furta.
Many, Yahweh my God, are the wonderful deeds that you have done, and your thoughts which are about us cannot be numbered; if I declared and spoke of them, they would be more than could be counted.
6 Hadaya da sadaka ba ka sha’awa, amma kunnuwana ka huda; hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka bukata.
You have no delight in sacrifice or offering, but you have opened my ears; you have not required burnt offerings or sin offerings.
7 Sa’an nan na ce, “Ga ni, na zo, kamar yadda yake a rubuce game da ni cikin littafi.
Then said I, “See, I have come; it is written about me in the scroll of the document.
8 Ina sha’awar aikata nufinka, ya Allahna; dokar tana cikin zuciyata.”
I delight to do your will, my God; your laws are in my heart.”
9 Na yi shelar adalcinka cikin babban taro; ba na rufe leɓunana, kamar yadda ka sani, ya Ubangiji.
I have proclaimed good news of your righteousness in the great assembly; Yahweh, you know that my lips have not kept back from doing this.
10 Ba na ɓoye adalcinka cikin zuciyata; ina maganar amincinka da cetonka. Ban ɓoye ƙaunarka da gaskiyarka a gaban taron jama’arka mai girma ba.
I have not concealed your righteousness in my heart; I have declared your faithfulness and your salvation; I have not concealed your covenant faithfulness or your trustworthiness from the great assembly.
11 Kada ka hana mini jinƙanka, ya Ubangiji; bari ƙaunarka da gaskiyarka kullum su kāre ni.
Do not keep back your acts of mercy from me, Yahweh; let your covenant faithfulness and your trustworthiness always preserve me.
12 Gama damuwoyin da suka wuce misali sun kewaye ni; zunubaina sun mamaye ni, kuma ba na iya gani. Sun fi gashin kaina yawa, har ma na fid da zuciya.
Troubles that cannot be numbered surround me; my iniquities have caught up with me so that I am no longer able to see anything; they are more than the hairs on my head, and my heart has failed me.
13 Ka ji daɗin cetona, ya Ubangiji; Ya Ubangiji, ka zo da sauri ka taimake ni.
Be pleased, Yahweh, to rescue me; hurry to help me, Yahweh.
14 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan waɗanda suke neman lalacewata su koma baya da kunya.
Let them be ashamed and completely disappointed who pursue my life to take it away. Let them be turned back and brought to dishonor, those who delight in hurting me.
15 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su sha mamaki saboda kunyar da za su sha.
Let them be shocked because of their shame, those who say to me, “Aha, aha!”
16 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Ubangiji mai girma ne!”
But may all those who seek you rejoice and be glad in you; let everyone who loves your salvation say continually, “May Yahweh be praised.”
17 Ni dai matalauci ne da mai bukata; bari Ubangiji yă tuna da ni. Kai ne taimakona da mai cetona; Ya Allahna, kada ka jinkirta.
I am poor and needy; yet the Lord thinks about me. You are my help and you come to my rescue; do not delay, my God.

< Zabura 40 >