< Zabura 40 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Na jira da haƙuri ga Ubangiji; ya juya wurina ya kuma ji kukata.
For the leader. A psalm of David. For the Lord I waited and waited, till, inclining to me, he heard my cry.
2 Ya ɗaga ni daga rami marar fāɗi, daga laka da taɓo; ya sa ƙafafuna a kan dutse ya kuma ba ni tsayayyen wuri don in tsaya.
From the horrible pit he drew me, up out of the miry clay; he set my feet on a rock, and my steps he made firm.
3 Ya sa sabuwar waƙa a bakina, waƙar yabo ga Allahna. Da yawa za su gani su tsorata su kuma dogara ga Ubangiji.
He put a new song in my mouth, of praise to our God. Many see it, and, filled with awe, put their trust in the Lord.
4 Mai albarka ne mutumin da ya mai da Ubangiji abin dogararsa, wanda ba ya kula da masu girman kai, waɗanda suka juya ga allolin ƙarya.
Happy the person who has put in the Lord their trust, not looking to false gods or turning to idols.
5 Da yawa ne, ya Ubangiji Allahna, abubuwan banmamakin da ka aikata. Abubuwan da ka shirya mana. Ba wanda zai iya faɗa maka su; a ce zan yi magana in faɗe su, za su wuce gaban misali a furta.
With us you have wrought in rich measure, O Lord our God, your marvels and purposes for us – none may compare with you – were I to declare or to tell them, past counting are they.
6 Hadaya da sadaka ba ka sha’awa, amma kunnuwana ka huda; hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka bukata.
In offerings bloody or bloodless you have no delight, but with open ears you have made me. Burnt-offering and offering for sin are not what you ask.
7 Sa’an nan na ce, “Ga ni, na zo, kamar yadda yake a rubuce game da ni cikin littafi.
Then said I, “Here I am, as the roll of the book has enjoined.
8 Ina sha’awar aikata nufinka, ya Allahna; dokar tana cikin zuciyata.”
My delight, O God, is to do your will, and your law is within my heart.”
9 Na yi shelar adalcinka cikin babban taro; ba na rufe leɓunana, kamar yadda ka sani, ya Ubangiji.
Well, O Lord, you know that, with lips unrestrained, your righteousness I told in the great congregation,
10 Ba na ɓoye adalcinka cikin zuciyata; ina maganar amincinka da cetonka. Ban ɓoye ƙaunarka da gaskiyarka a gaban taron jama’arka mai girma ba.
not hiding it in my heart. I have told of your steadfast help, from the great congregation I hid not your love and your faithfulness.
11 Kada ka hana mini jinƙanka, ya Ubangiji; bari ƙaunarka da gaskiyarka kullum su kāre ni.
So do not restrain, Lord, your pity from us. Your love and your faithfulness – ever may they be our shield.
12 Gama damuwoyin da suka wuce misali sun kewaye ni; zunubaina sun mamaye ni, kuma ba na iya gani. Sun fi gashin kaina yawa, har ma na fid da zuciya.
For evils that cannot be numbered have compassed me round. My transgressions have followed me up – I can bear it no more. They are more than the hairs of my head, and my heart has forsaken me.
13 Ka ji daɗin cetona, ya Ubangiji; Ya Ubangiji, ka zo da sauri ka taimake ni.
O Lord, be pleased to deliver me, haste to my help, O Lord.
14 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan waɗanda suke neman lalacewata su koma baya da kunya.
May those who are seeking my life be ashamed and confounded together; may those who delight in my hurt be defeated and brought to dishonor.
15 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su sha mamaki saboda kunyar da za su sha.
May those who hurrah over me be dumbfounded because of their shame.
16 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Ubangiji mai girma ne!”
But may all who seek after you rejoice and be glad in you. May all those eager for your aid, say, “Great is the Lord” evermore.
17 Ni dai matalauci ne da mai bukata; bari Ubangiji yă tuna da ni. Kai ne taimakona da mai cetona; Ya Allahna, kada ka jinkirta.
I am weak and needy, yet the Lord cares for me. You are my help and deliverer; don’t delay, my God.