< Zabura 40 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Na jira da haƙuri ga Ubangiji; ya juya wurina ya kuma ji kukata.
For the Chief Musician. A Psalm of David. I waited patiently for Jehovah; And he inclined unto me, and heard my cry.
2 Ya ɗaga ni daga rami marar fāɗi, daga laka da taɓo; ya sa ƙafafuna a kan dutse ya kuma ba ni tsayayyen wuri don in tsaya.
He brought me up also out of a horrible pit, out of the miry clay; And he set my feet upon a rock, and established my goings.
3 Ya sa sabuwar waƙa a bakina, waƙar yabo ga Allahna. Da yawa za su gani su tsorata su kuma dogara ga Ubangiji.
And he hath put a new song in my mouth, even praise unto our God: Many shall see it, and fear, And shall trust in Jehovah.
4 Mai albarka ne mutumin da ya mai da Ubangiji abin dogararsa, wanda ba ya kula da masu girman kai, waɗanda suka juya ga allolin ƙarya.
Blessed is the man that maketh Jehovah his trust, And respecteth not the proud, nor such as turn aside to lies.
5 Da yawa ne, ya Ubangiji Allahna, abubuwan banmamakin da ka aikata. Abubuwan da ka shirya mana. Ba wanda zai iya faɗa maka su; a ce zan yi magana in faɗe su, za su wuce gaban misali a furta.
Many, O Jehovah my God, are the wonderful works which thou hast done, And thy thoughts which are to us-ward: They cannot be set in order unto thee; If I would declare and speak of them, They are more than can be numbered.
6 Hadaya da sadaka ba ka sha’awa, amma kunnuwana ka huda; hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka bukata.
Sacrifice and offering thou hast no delight in; Mine ears hast thou opened: Burnt-offering and sin-offering hast thou not required.
7 Sa’an nan na ce, “Ga ni, na zo, kamar yadda yake a rubuce game da ni cikin littafi.
Then said I, Lo, I am come; In the roll of the book it is written of me:
8 Ina sha’awar aikata nufinka, ya Allahna; dokar tana cikin zuciyata.”
I delight to do thy will, O my God; Yea, thy law is within my heart.
9 Na yi shelar adalcinka cikin babban taro; ba na rufe leɓunana, kamar yadda ka sani, ya Ubangiji.
I have proclaimed glad tidings of righteousness in the great assembly; Lo, I will not refrain my lips, O Jehovah, thou knowest.
10 Ba na ɓoye adalcinka cikin zuciyata; ina maganar amincinka da cetonka. Ban ɓoye ƙaunarka da gaskiyarka a gaban taron jama’arka mai girma ba.
I have not hid thy righteousness within my heart; I have declared thy faithfulness and thy salvation; I have not concealed thy lovingkindness and thy truth from the great assembly.
11 Kada ka hana mini jinƙanka, ya Ubangiji; bari ƙaunarka da gaskiyarka kullum su kāre ni.
Withhold not thou thy tender mercies from me, O Jehovah; Let thy lovingkindness and thy truth continually preserve me.
12 Gama damuwoyin da suka wuce misali sun kewaye ni; zunubaina sun mamaye ni, kuma ba na iya gani. Sun fi gashin kaina yawa, har ma na fid da zuciya.
For innumerable evils have compassed me about; Mine iniquities have overtaken me, so that I am not able to look up; They are more than the hairs of my head; And my heart hath failed me.
13 Ka ji daɗin cetona, ya Ubangiji; Ya Ubangiji, ka zo da sauri ka taimake ni.
Be pleased, O Jehovah, to deliver me: Make haste to help me, O Jehovah.
14 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan waɗanda suke neman lalacewata su koma baya da kunya.
Let them be put to shame and confounded together That seek after my soul to destroy it: Let them be turned backward and brought to dishonor That delight in my hurt.
15 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su sha mamaki saboda kunyar da za su sha.
Let them be desolate by reason of their shame That say unto me, Aha, aha.
16 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Ubangiji mai girma ne!”
Let all those that seek thee rejoice and be glad in thee: Let such as love thy salvation say continually, Jehovah be magnified.
17 Ni dai matalauci ne da mai bukata; bari Ubangiji yă tuna da ni. Kai ne taimakona da mai cetona; Ya Allahna, kada ka jinkirta.
But I am poor and needy; [Yet] the Lord thinketh upon me: Thou art my help and my deliverer; Make no tarrying, O my God.

< Zabura 40 >