< Zabura 4 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
Poslušaj me, kadar kličem, oh Bog moje pravičnosti. Osvobodil si me, ko sem bil v stiski, usmili se me in usliši mojo molitev.
2 Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
Oh vi človeški sinovi, doklej boste mojo slavo spreminjali v sramoto? Kako dolgo boste ljubili prazne reči in iskali laž? (Sela)
3 Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
Toda vedite, da je Gospod zase oddvojil tistega, ki je bogaboječ. Gospod bo slišal, kadar kličem k njemu.
4 Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
Stoj v strahospoštovanju in ne greši. Na svoji postelji se posvetuj s svojim lastnim srcem in miruj. (Sela)
5 Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
Daruj klavne daritve pravičnosti in svoje trdno upanje položi v Gospoda.
6 Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
Mnogi so, ki pravijo: »Kdo nam bo pokazal karkoli dobrega?« Gospod, dvigni nad nami svetlobo svojega obličja.
7 Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
V moje srce si položil veselje, več kot v času, ko je naraslo njihovo žito in njihovo vino.
8 Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.
V miru se bom ulegel in spal. Kajti samo ti, Gospod, mi daješ prebivati na varnem.