< Zabura 4 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
Ngiphendula ekukhaleni kwami, Nkulunkulu wokulunga kwami. Ekucindezelweni wangenzela indawo ebanzi. Woba lomusa kimi, uzwe umkhuleko wami.
2 Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
Madodana abantu, koze kube nini liphendula udumo lwami lube lihlazo, lithanda okuyize, lidinga amanga? (Sela)
3 Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
Kodwa yazini ukuthi iNkosi izehlukanisele owesaba uNkulunkulu; iNkosi iyangizwa lapho ngikhala kuyo.
4 Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
Thuthumelani, lingoni; khulumani lenhliziyo yenu embhedeni wenu, lithule. (Sela)
5 Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
Nikelani imihlatshelo yokulunga, lithembe eNkosini.
6 Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
Banengi abathi: Ngubani ozasitshengisa okuhle? Nkosi, phakamisela ukukhanya kobuso bakho phezu kwethu.
7 Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
Ubeke intokozo enhliziyweni yami okwedlula isikhathi lapho amabele abo lewayini labo elitsha kwandile.
8 Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.
Ngizacambalala ngokuthula, khonokho ngilale ubuthongo, ngoba wena Nkosi wedwa uyangihlalisa ngokulondolozeka.

< Zabura 4 >