< Zabura 4 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
Dem Sangmeister, mit Saitenspielbegleitung. Ein Psalm Davids.
2 Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
Wenn ich rufe, erhöre mich, Gott meines Heils! / Du hast mich ja schon aus Drangsal errettet; / So sei mir nun gnädig und hör mein Gebet!
3 Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
Ihr Männer von Ansehn, wie lange wollt ihr meine Ehre schänden, / Indem ihr das Nichtige liebt und auf Lügen sinnt? (Sela)
4 Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
Wisset, daß Jahwe mich reich begnadet: Jahwe hört, wenn ich zu ihm rufe.
5 Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
Wollt ihr zürnen, so sündigt doch nicht! / Prüft euer Herz im stillen und schweigt! (Sela)
6 Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
Bringt rechte Opfer und traut auf Jahwe!
7 Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
Viele sagen: "Wer läßt uns Gutes schaun?" / O, erheb über uns das Licht deines Angesichts, Jahwe!
8 Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.
Du hast mir Freude ins Herz gegeben; / Das ist ein besserer Schatz als all ihr Korn und Most. Nun will ich in Frieden mich niederlegen zum Schlaf; / Denn du, o Jahwe, lässest mich ungestört und sicher wohnen.

< Zabura 4 >