< Zabura 4 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
Quand je crie, réponds-moi, ô Dieu de ma justice! Quand j'étais à l'étroit, tu m'as mis au large; aie pitié de moi, entends ma prière!
2 Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
Fils des hommes, jusques à quand ma gloire sera-t-elle mise en opprobre? Jusques à quand aimerez-vous la vanité, et rechercherez-vous le mensonge? (Sélah)
3 Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
Sachez que l'Éternel s'est choisi un bien-aimé. L'Éternel m'entend quand je crie à lui.
4 Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
Tremblez, et ne péchez point! Parlez en vos cœurs sur votre couche, et gardez le silence! (Sélah)
5 Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
Offrez des sacrifices de justice, et confiez-vous en l'Éternel.
6 Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
Plusieurs disent: Qui nous fera voir du bien? Fais lever sur nous la lumière de ta face, ô Éternel!
7 Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
Tu as mis dans mon cœur plus de joie, qu'ils n'en ont quand leur blé et leur vin sont abondants.
8 Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.
Je me coucherai, je m'endormirai aussi en paix; car toi seul, ô Éternel, tu me fais reposer en assurance.