< Zabura 4 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
Jusqu'à la Fin, un cantique de David dans les Psaumes. Lorsque je l'eus invoqué, le Dieu de ma justice, il m'exauça; tu m'as dilaté en mon affliction. Aie pitié de moi, et exauce ma prière!
2 Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
Fils des hommes, jusques à quand aurez-vous le cœur appesanti? D'où vient que tous aimez la vanité, et cherchez le mensonge? Interlude.
3 Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
Sachez donc que le Seigneur a rendu son Saint admirable; le Seigneur m'exaucera, lorsque je crierai vers lui.
4 Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
Indignez-vous, mais ne péchez pas; soyez touchés de componction de ce que vous méditez sur votre couche au fond de vos cœurs. Interlude.
5 Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
Offrez le sacrifice de justice, et espérez au Seigneur;
6 Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
Plusieurs disent: Qui nous fera voir les biens? Seigneur, la lumière de ta face est empreinte sur nous;
7 Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
Tu as mis la joie dans mon cœur. [Mes ennemis] se sont multipliés dans l'abondance de leur pain, de leur vin, de leur huile.
8 Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.
Pour moi, je m'endormirai et me reposerai dans la paix; parce que toi, Seigneur, par une grâce singulière, tu m'as établi dans l'espérance.