< Zabura 4 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
`To the victorie in orguns; the salm of Dauid. Whanne Y inwardli clepid, God of my riytwisnesse herde me; in tribulacioun thou hast alargid to me.
2 Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
Haue thou mercy on me; and here thou my preier. Sones of men, hou long ben ye of heuy herte? whi louen ye vanite, and seken a leesyng?
3 Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
And wite ye, that the Lord hath maad merueilous his hooli man; the Lord schal here me, whanne Y schal crye to hym.
4 Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
Be ye wrothe, and nyle ye do synne; `and for tho thingis whiche ye seien in youre hertis and in youre beddis, be ye compunct.
5 Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
Sacrifie ye `the sacrifice of riytfulnesse, and hope ye in the Lord; many seien, Who schewide goodis to vs?
6 Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
Lord, the liyt of thi cheer is markid on vs; thou hast youe gladnesse in myn herte.
7 Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
Thei ben multiplied of the fruit of whete, and of wyn; and of her oile.
8 Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.
In pees in the same thing; Y schal slepe, and take reste. For thou, Lord; hast set me syngulerli in hope.