< Zabura 4 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
For the Chief Musician; on stringed instruments. A Psalm of David. Answer me when I call, O God of my righteousness; thou hast set me at large [when I was] in distress: have mercy upon me, and hear my prayer.
2 Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
O ye sons of men, how long shall my glory be turned into dishonour? [how long] will ye love vanity, and seek after falsehood? (Selah)
3 Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
But know that the LORD hath set apart him that is godly for himself: the LORD will hear when I call unto him.
4 Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
Stand in awe, and sin not: commune with your own heart upon your bed, and be still. (Selah)
5 Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
Offer the sacrifices of righteousness, and put your trust in the LORD.
6 Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
Many there be that say, Who will shew us [any] good? LORD, lift thou up the light of thy countenance upon us.
7 Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
Thou hast put gladness in my heart, more than [they have] when their corn and their wine are increased.
8 Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.
In peace will I both lay me down and sleep: for thou, LORD, alone makest me dwell in safety.

< Zabura 4 >