< Zabura 4 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
For the leader, with stringed instruments. A psalm of David. Answer my cry, God, my defender. Often from straits you have brought me to spacious places. So now show me your favor and hear my prayer.
2 Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
How long, you proud people, will my honor be stained by the slanders you love, and the lies that you follow? (Selah)
3 Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
See! The Lord has shown me his wonderful kindness: the Lord hears, when I call to him.
4 Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
Sin not in your anger: but speak in your heart on your bed, and be still. (Selah)
5 Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
Offer true sacrifice, trust in the Lord.
6 Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
Many are longing for fortune to smile. Lift upon us the light of your face.
7 Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
You have put in my heart, Lord, a deeper joy than was theirs who had corn and wine in abundance.
8 Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.
So in peace I will lie down and sleep; for you, Lord, keep me safe.

< Zabura 4 >