< Zabura 4 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
“For the leader of the music; to be accompanied with stringed instruments. A psalm of David.” Hear me, when I call, O God of my righteousness! Thou hast helped me, when I was in trouble, —Have pity upon me, and hear my prayer!
2 Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
How long, O men! will ye dishonor my dignity? How long will ye love vanity, and seek disappointment? (Pause)
3 Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
Know ye that the LORD hath exalted one that is devoted to him; The LORD will hear, when I call upon him.
4 Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
Stand in awe, and sin no more; Commune with your hearts upon your beds, and desist! (Pause)
5 Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
Offer sacrifices of righteousness, And put your trust in the LORD!
6 Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
There are many who say, Who will show us any good? LORD, lift thou up the light of thy countenance upon us!
7 Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
Thou puttest gladness into my heart, Greater than theirs, when their corn and wine are abundant.
8 Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.
I will lay me down in peace, and sleep: For thou alone, O LORD! makest me dwell in safety.