< Zabura 4 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
TO THE OVERSEER. WITH STRINGED INSTRUMENTS. A PSALM OF DAVID. In my calling answer me, O God of my righteousness. In adversity You gave enlargement to me; Favor me, and hear my prayer.
2 Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
Sons of men! Until when [is] my glory for shame? You love a vain thing, you seek a lie. (Selah)
3 Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
And know that YHWH Has separated a saintly one to Himself. YHWH hears in my calling to Him.
4 Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
“Tremble, and do not sin”; Say [thus] in your heart on your bed, And be silent. (Selah)
5 Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
Sacrifice sacrifices of righteousness, And trust in YHWH.
6 Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
Many are saying, “Who shows us good?” Lift on us the light of Your face, O YHWH,
7 Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
You have given joy in my heart, From the time their grain and their wine Have been multiplied.
8 Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.
Together I lie down and sleep in peace, For You, O YHWH, alone, Cause me to dwell in confidence!

< Zabura 4 >