< Zabura 4 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
For the Leader; with string-music. A Psalm of David. Answer me when I call, O God of my righteousness, Thou who didst set me free when I was in distress; be gracious unto me, and hear my prayer.
2 Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
O ye sons of men, how long shall my glory be put to shame, in that ye love vanity, and seek after falsehood? (Selah)
3 Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
But know that the LORD hath set apart the godly man as His own; the LORD will hear when I call unto Him.
4 Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
Tremble, and sin not; commune with your own heart upon your bed, and be still. (Selah)
5 Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
Offer the sacrifices of righteousness, and put your trust in the LORD.
6 Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
Many there are that say: 'Oh that we could see some good!' LORD, lift Thou up the light of Thy countenance upon us.
7 Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
Thou hast put gladness in my heart, more than when their corn and their wine increase.
8 Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.
In peace will I both lay me down and sleep; for Thou, LORD, makest me dwell alone in safety.