< Zabura 39 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zabura ta Dawuda. Na ce, “Zan lura da hanyoyina zan kuma kiyaye harshena daga zunubi; zan sa linzami a bakina muddin mugaye suna a gabana.”
Rekel sem: »Pazil bom na svoje poti, da ne bom grešil s svojim jezikom. Ko bo zlobni pred menoj, bom svoja usta držal z uzdo.«
2 Na yi shiru, ban ce kome ba, Ko a kan abin da yake da kyau! Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi;
Bil sem nem s tišino, molčal sem, celó pred dobrim in moja bridkost je bila razvneta.
3 zuciyata ta ƙara zafi a cikina. Kuma sa’ad da nake tunani, wuta ta yi ta kuna; sai na yi magana da harshena na ce,
Moje srce je bilo vroče znotraj mene, medtem ko sem razglabljal, je zagorel ogenj, potem sem spregovoril s svojim jezikom:
4 “Nuna mini, ya Ubangiji, ƙarshen rayuwata da kuma yawan kwanakina; bari in san yadda rayuwata tana wucewa da sauri.
» Gospod, daj mi spoznati moj konec in mero mojih dni, kolikšna je, da lahko spoznam, kako slaboten sem.
5 Ka sa kwanakina suka zama tafin hannu ne kawai; yawan shekaruna kamar ba kome ba ne a gabanka. Duk ran mutum shaƙar iska ne kurum, har ma waɗanda suke tsammani suke da kāriya. (Sela)
Glej, moje dneve si naredil kakor dlan in moja starost je kakor nič pred teboj. Resnično, vsak človek v svojem najboljšem stanju je povsem ničevost.« (Sela)
6 “Mutum dai shirim ne kawai yayinda yake kai da komowa. Yana ta yawo, amma a banza ne kawai; yakan tara dukiya, ba tare da sanin wa zai more ta ba.
Zagotovo vsak človek hodi v prazni podobi, zagotovo so zaman vznemirjeni. Kopiči bogastva, pa ne ve, kdo jih bo pobral.
7 “Amma yanzu, ya Ubangiji, me zan nema? Begena yana a gare ka.
In sedaj, Gospod, kaj [naj] pričakujem? Moje upanje je v tebi.
8 Ka cece ni daga dukan laifofina; kada ka sa in zama abin dariya ga wawaye.
Osvobodi me pred vsemi mojimi prestopki. Ne naredi me [za] grajo nespametnim.
9 Na yi shiru; ba zan buɗe bakina ba, gama kai ne wanda ka aikata wannan.
Bil sem nem, svojih ust nisem odprl, ker si ti to storil.
10 Ka ɗauke bulalarka daga gare ni; na ji jiki ta wurin bugun da hannunka ya yi mini.
Umakni svoj udarec proč od mene. Použit sem z zamahom tvoje roke.
11 Kakan tsawata ka kuma hore mutane saboda zunubinsu; kakan cinye wadatarsu kamar yadda asu ke yi, kowane mutum dai shaƙar iska ne. (Sela)
Kadar za krivičnost z grajanjem korigiraš človeka, storiš, da njegova lepota shira kakor molj. Zagotovo je vsak človek ničevost. (Sela)
12 “Ka ji addu’ata, ya Ubangiji, ka saurari kukata ta neman taimako; kada ka kurmance ga kukata. Gama ina zama tare da kai kamar baƙo, baƙo, kamar yadda dukan kakannina sun kasance.
Usliši mojo molitev, oh Gospod in pazljivo prisluhni mojemu vpitju; ob mojih solzah ne molči. Kajti jaz sem tujec s teboj in začasni prebivalec, kakor so bili vsi moji očetje.
13 Ka kau da fuskarka daga gare ni, saboda in sāke yin farin ciki kafin in tafi in kuma rabu da nan.”
Oh prizanesi mi, da lahko obnovim moč, preden grem naprej in ne bom več.