< Zabura 39 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zabura ta Dawuda. Na ce, “Zan lura da hanyoyina zan kuma kiyaye harshena daga zunubi; zan sa linzami a bakina muddin mugaye suna a gabana.”
Para o músico chefe. Para Jeduthun. Um Salmo de David. I disse: “Vou vigiar meus caminhos, para não pecar com minha língua. Eu manterei minha boca com uma cabeçada enquanto o maligno estiver diante de mim”.
2 Na yi shiru, ban ce kome ba, Ko a kan abin da yake da kyau! Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi;
Eu fiquei mudo com o silêncio. Eu me calei, mesmo do bem. Meu pesar foi despertado.
3 zuciyata ta ƙara zafi a cikina. Kuma sa’ad da nake tunani, wuta ta yi ta kuna; sai na yi magana da harshena na ce,
My o coração estava quente dentro de mim. Enquanto eu meditava, o fogo ardeu. Falei com minha língua:
4 “Nuna mini, ya Ubangiji, ƙarshen rayuwata da kuma yawan kwanakina; bari in san yadda rayuwata tana wucewa da sauri.
“Yahweh, mostre-me o meu fim, qual é a medida dos meus dias. Me informe o quão frágil eu sou.
5 Ka sa kwanakina suka zama tafin hannu ne kawai; yawan shekaruna kamar ba kome ba ne a gabanka. Duk ran mutum shaƙar iska ne kurum, har ma waɗanda suke tsammani suke da kāriya. (Sela)
Behold, você fez meus dias larguras de mão. Minha vida é como nada diante de vocês. Certamente todo homem está de pé como um sopro”. (Selah)
6 “Mutum dai shirim ne kawai yayinda yake kai da komowa. Yana ta yawo, amma a banza ne kawai; yakan tara dukiya, ba tare da sanin wa zai more ta ba.
“Certamente todo homem caminha como uma sombra. Certamente, eles se ocupam em vão. Ele se amontoa e não sabe quem deve se reunir.
7 “Amma yanzu, ya Ubangiji, me zan nema? Begena yana a gare ka.
Agora, Senhor, o que eu espero? Minha esperança está em você.
8 Ka cece ni daga dukan laifofina; kada ka sa in zama abin dariya ga wawaye.
Deliver me de todas as minhas transgressões. Não me faça censurar os tolos.
9 Na yi shiru; ba zan buɗe bakina ba, gama kai ne wanda ka aikata wannan.
Eu era mudo. Eu não abri minha boca, porque você o fez.
10 Ka ɗauke bulalarka daga gare ni; na ji jiki ta wurin bugun da hannunka ya yi mini.
Tire seu flagelo de perto de mim. Estou dominado pelo golpe de sua mão.
11 Kakan tsawata ka kuma hore mutane saboda zunubinsu; kakan cinye wadatarsu kamar yadda asu ke yi, kowane mutum dai shaƙar iska ne. (Sela)
Quando você repreende e corrige o homem por iniqüidade, você consome sua riqueza como uma traça. Certamente todo homem é apenas um sopro”. (Selah)
12 “Ka ji addu’ata, ya Ubangiji, ka saurari kukata ta neman taimako; kada ka kurmance ga kukata. Gama ina zama tare da kai kamar baƙo, baƙo, kamar yadda dukan kakannina sun kasance.
“Ouça minha oração, Yahweh, e dê ouvidos ao meu choro. Não fique em silêncio diante das minhas lágrimas. Pois eu sou um estranho com você, um estrangeiro, como todos os meus pais foram.
13 Ka kau da fuskarka daga gare ni, saboda in sāke yin farin ciki kafin in tafi in kuma rabu da nan.”
Oh me poupe, para que eu possa recuperar minhas forças, antes que eu vá embora e não exista mais”.