< Zabura 39 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zabura ta Dawuda. Na ce, “Zan lura da hanyoyina zan kuma kiyaye harshena daga zunubi; zan sa linzami a bakina muddin mugaye suna a gabana.”
Dāvida dziesma, dziedātāju vadonim, Jedutunam. Es esmu apņēmies, ka savu ceļu sargāšu, ka negrēkošu ar savu mēli; es sargāšu savu muti kā ar iemauktiem, kamēr bezdievīgais manā priekšā.
2 Na yi shiru, ban ce kome ba, Ko a kan abin da yake da kyau! Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi;
Es esmu palicis kā mēms un klusu cietis, un nepieminu vairs labuma, bet manas sāpes vairojās.
3 zuciyata ta ƙara zafi a cikina. Kuma sa’ad da nake tunani, wuta ta yi ta kuna; sai na yi magana da harshena na ce,
Mana sirds ir iekarsusi iekš manis; kad es uz to domāju, tad es iedegos kā uguns; es runāju ar savu mēli:
4 “Nuna mini, ya Ubangiji, ƙarshen rayuwata da kuma yawan kwanakina; bari in san yadda rayuwata tana wucewa da sauri.
Kungs, māci man manu galu un kāds ir manu dienu mērs, lai es zinu, cik nīcīgs es esmu.
5 Ka sa kwanakina suka zama tafin hannu ne kawai; yawan shekaruna kamar ba kome ba ne a gabanka. Duk ran mutum shaƙar iska ne kurum, har ma waɗanda suke tsammani suke da kāriya. (Sela)
Redzi, Tu manas dienas esi licis plaukstas platumā, un mans mūžs ir kā nekas Tavā priekšā; tiešām niecība vien ir ikviens cilvēks savā stiprumā. (Sela)
6 “Mutum dai shirim ne kawai yayinda yake kai da komowa. Yana ta yawo, amma a banza ne kawai; yakan tara dukiya, ba tare da sanin wa zai more ta ba.
Cilvēks staigā kā ēna un nieka dēļ raizējās; viņš krāj, bet nezin, kas to dabūs.
7 “Amma yanzu, ya Ubangiji, me zan nema? Begena yana a gare ka.
Nu tad, uz ko man būs gaidīt, Kungs? Es cerēju uz Tevi.
8 Ka cece ni daga dukan laifofina; kada ka sa in zama abin dariya ga wawaye.
Izglāb mani no visām manām pārkāpšanām, un neliec man ģeķiem palikt par apsmieklu.
9 Na yi shiru; ba zan buɗe bakina ba, gama kai ne wanda ka aikata wannan.
Es esmu klusu un neatdaru savu muti; jo Tu to esi darījis.
10 Ka ɗauke bulalarka daga gare ni; na ji jiki ta wurin bugun da hannunka ya yi mini.
Atņem Savu mocību no manis, jo es nīkstu no Tavas rokas grūtuma.
11 Kakan tsawata ka kuma hore mutane saboda zunubinsu; kakan cinye wadatarsu kamar yadda asu ke yi, kowane mutum dai shaƙar iska ne. (Sela)
Kad Tu cilvēku pārmāci par noziegumiem, tad Tu iznīcini viņa skaistumu kā kodes; tiešām: visi cilvēki ir niecība.(Sela.)
12 “Ka ji addu’ata, ya Ubangiji, ka saurari kukata ta neman taimako; kada ka kurmance ga kukata. Gama ina zama tare da kai kamar baƙo, baƙo, kamar yadda dukan kakannina sun kasance.
Klausi, Kungs, manu lūgšanu, ņem vērā manu saukšanu, un neciet klusu pie manām asarām, jo es esmu svešinieks un piedzīvotājs Tavā priekšā, tā kā visi mani tēvi.
13 Ka kau da fuskarka daga gare ni, saboda in sāke yin farin ciki kafin in tafi in kuma rabu da nan.”
Atstājies no manis, ka es atspirgstos, pirms noeju un vairs neesmu.