< Zabura 39 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zabura ta Dawuda. Na ce, “Zan lura da hanyoyina zan kuma kiyaye harshena daga zunubi; zan sa linzami a bakina muddin mugaye suna a gabana.”
[Psalm lal David] Nga fahk, “Nga fah karinganang ma nga oru Ac tia lela tuh louk in aktafongyeyula; Nga fah tia fahk kutena ma Ke pacl mwet koluk elos muta apkuran.”
2 Na yi shiru, ban ce kome ba, Ko a kan abin da yake da kyau! Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi;
Nga mislana, ac tia fahk kutena kas, Finne ke ma wo, nga tia pac kaskas. Tusruktu keok luk yokyokelik,
3 zuciyata ta ƙara zafi a cikina. Kuma sa’ad da nake tunani, wuta ta yi ta kuna; sai na yi magana da harshena na ce,
Ac fosrnga uh kutangyula. Ke nga srike in nunku ma inge, na upala fohs luk, Pwanang nga tia ku in misla in siyuk,
4 “Nuna mini, ya Ubangiji, ƙarshen rayuwata da kuma yawan kwanakina; bari in san yadda rayuwata tana wucewa da sauri.
“LEUM GOD, nga ac moul putaka? Nga ac misa ngac? Fahk nu sik lah moul luk uh ac safla ngac.”
5 Ka sa kwanakina suka zama tafin hannu ne kawai; yawan shekaruna kamar ba kome ba ne a gabanka. Duk ran mutum shaƙar iska ne kurum, har ma waɗanda suke tsammani suke da kāriya. (Sela)
Kom orala moul luk arulana fototo! Lusen moul luk ye motom oana ma wangin. Pwayena lah lusen moul lun mwet se oana momong na fototo se.
6 “Mutum dai shirim ne kawai yayinda yake kai da komowa. Yana ta yawo, amma a banza ne kawai; yakan tara dukiya, ba tare da sanin wa zai more ta ba.
El sarla oana lul se. Ma nukewa el oru wangin sripa; El akpusye mwe kasrup lal, ac tia etu lah su ac mau eis.
7 “Amma yanzu, ya Ubangiji, me zan nema? Begena yana a gare ka.
O Leum, mea nga ku in finsrak nu kac? Nga filiya finsrak luk in kom.
8 Ka cece ni daga dukan laifofina; kada ka sa in zama abin dariya ga wawaye.
Moliyula liki ma koluk luk nukewa, Ac nikmet lela tuh mwet lalfon in aksruksrukyeyu.
9 Na yi shiru; ba zan buɗe bakina ba, gama kai ne wanda ka aikata wannan.
Nga ac mutana misla; nga ac fah tiana fahk sie kas, Mweyen kom pa oru nga keok ouinge uh.
10 Ka ɗauke bulalarka daga gare ni; na ji jiki ta wurin bugun da hannunka ya yi mini.
Nikmet sifil akkeokyeyu, Tuh nga apkuran in misa ke sringsring lom!
11 Kakan tsawata ka kuma hore mutane saboda zunubinsu; kakan cinye wadatarsu kamar yadda asu ke yi, kowane mutum dai shaƙar iska ne. (Sela)
Kom sang kas in kai nu sin sie mwet ke sripen ma koluk lal, Na, oana sie watil, kom kunausla ma el lungse yohk. Aok, moul lun mwet uh oana momong na fototo se.
12 “Ka ji addu’ata, ya Ubangiji, ka saurari kukata ta neman taimako; kada ka kurmance ga kukata. Gama ina zama tare da kai kamar baƙo, baƙo, kamar yadda dukan kakannina sun kasance.
O LEUM GOD, lohng pre luk, Porongo tung luk; Ase kasru lom nu sik ke pacl nga tung. Nga oana sie mwetsac su mutwata yurum ke kitin pacl na, Oana mwet matu nukewa luk somla ah.
13 Ka kau da fuskarka daga gare ni, saboda in sāke yin farin ciki kafin in tafi in kuma rabu da nan.”
Fahla likiyu, nga in mau ku in engan kutu srisrik Meet liki nga som ac wanginla.