< Zabura 39 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zabura ta Dawuda. Na ce, “Zan lura da hanyoyina zan kuma kiyaye harshena daga zunubi; zan sa linzami a bakina muddin mugaye suna a gabana.”
Au maître chantre des Jéduthunites. Cantique de David. J'avais dit: « Je veillerai sur mes voies, pour ne point pécher par la langue; j'aurai soin de mettre un frein à ma bouche, tant que les impies seront en ma présence. »
2 Na yi shiru, ban ce kome ba, Ko a kan abin da yake da kyau! Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi;
Je fus muet, silencieux, évitant même de parler du bonheur. Mais ma douleur s'irritait,
3 zuciyata ta ƙara zafi a cikina. Kuma sa’ad da nake tunani, wuta ta yi ta kuna; sai na yi magana da harshena na ce,
mon cœur s'enflammait dans mon sein, où mes pensées allumèrent un feu, et ma langue parla.
4 “Nuna mini, ya Ubangiji, ƙarshen rayuwata da kuma yawan kwanakina; bari in san yadda rayuwata tana wucewa da sauri.
Éternel, montre-moi le terme de ma vie, et quelle est la durée de mes jours! O! que je sache combien je suis fragile!
5 Ka sa kwanakina suka zama tafin hannu ne kawai; yawan shekaruna kamar ba kome ba ne a gabanka. Duk ran mutum shaƙar iska ne kurum, har ma waɗanda suke tsammani suke da kāriya. (Sela)
Voici, tu as donné à mes jours l'espace d'une palme, et ma durée est comme un néant devant toi; oui, tout homme a la consistance d'un souffle. (Pause)
6 “Mutum dai shirim ne kawai yayinda yake kai da komowa. Yana ta yawo, amma a banza ne kawai; yakan tara dukiya, ba tare da sanin wa zai more ta ba.
Oui, comme une ombre le mortel se promène; oui, il s'agite avec bruit pour ce qui passe; il amasse, et il ne sait qui recueillera.
7 “Amma yanzu, ya Ubangiji, me zan nema? Begena yana a gare ka.
Et maintenant, que puis-je attendre, Seigneur? Mon espoir est en toi.
8 Ka cece ni daga dukan laifofina; kada ka sa in zama abin dariya ga wawaye.
Sauve-moi de tous mes péchés, ne m'expose pas aux outrages de l'impie!
9 Na yi shiru; ba zan buɗe bakina ba, gama kai ne wanda ka aikata wannan.
Mais je me tais, je n'ouvre pas la bouche, car c'est toi qui agis.
10 Ka ɗauke bulalarka daga gare ni; na ji jiki ta wurin bugun da hannunka ya yi mini.
Eloigne de moi tes plaies! Je péris sous ta main irritée.
11 Kakan tsawata ka kuma hore mutane saboda zunubinsu; kakan cinye wadatarsu kamar yadda asu ke yi, kowane mutum dai shaƙar iska ne. (Sela)
Quand par des peines tu châties l'homme d'une faute, semblable à la teigne, tu détruis son bien le plus cher. Oui, tout mortel est un souffle. (Pause)
12 “Ka ji addu’ata, ya Ubangiji, ka saurari kukata ta neman taimako; kada ka kurmance ga kukata. Gama ina zama tare da kai kamar baƙo, baƙo, kamar yadda dukan kakannina sun kasance.
Ecoute ma prière, Éternel, et prête l'oreille à mes cris! Ne sois point sourd à mes larmes, car je suis un étranger chez toi, un hôte, comme tous mes pères!
13 Ka kau da fuskarka daga gare ni, saboda in sāke yin farin ciki kafin in tafi in kuma rabu da nan.”
Ne tiens plus tes yeux attachés sur moi, afin que je retrouve la sérénité, avant que je m'en aille, et que je ne sois plus!

< Zabura 39 >