< Zabura 39 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zabura ta Dawuda. Na ce, “Zan lura da hanyoyina zan kuma kiyaye harshena daga zunubi; zan sa linzami a bakina muddin mugaye suna a gabana.”
Pour le chef musicien. Pour Jeduthun. Un psaume de David. J'ai dit: « Je veillerai sur mes voies, afin de ne pas pécher par ma langue. Je tiendrai ma bouche en bride tant que le méchant sera devant moi. »
2 Na yi shiru, ban ce kome ba, Ko a kan abin da yake da kyau! Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi;
Je suis resté muet de silence. J'ai gardé la paix, même avec le bien. Mon chagrin a été remué.
3 zuciyata ta ƙara zafi a cikina. Kuma sa’ad da nake tunani, wuta ta yi ta kuna; sai na yi magana da harshena na ce,
Mon cœur était brûlant au-dedans de moi. Pendant que je méditais, le feu brûlait. J'ai parlé avec ma langue:
4 “Nuna mini, ya Ubangiji, ƙarshen rayuwata da kuma yawan kwanakina; bari in san yadda rayuwata tana wucewa da sauri.
« Yahvé, montre-moi ma fin, quelle est la mesure de mes jours. Faites-moi savoir à quel point je suis fragile.
5 Ka sa kwanakina suka zama tafin hannu ne kawai; yawan shekaruna kamar ba kome ba ne a gabanka. Duk ran mutum shaƙar iska ne kurum, har ma waɗanda suke tsammani suke da kāriya. (Sela)
Voici, tu as fait de mes jours des largeurs de main. Ma vie n'est rien devant vous. Chaque homme est comme un souffle. (Selah)
6 “Mutum dai shirim ne kawai yayinda yake kai da komowa. Yana ta yawo, amma a banza ne kawai; yakan tara dukiya, ba tare da sanin wa zai more ta ba.
« Certes, tout homme marche comme une ombre. Ils s'occupent en vain. Il amasse, et ne sait pas qui va ramasser.
7 “Amma yanzu, ya Ubangiji, me zan nema? Begena yana a gare ka.
Maintenant, Seigneur, qu'est-ce que j'attends? Mon espoir est en vous.
8 Ka cece ni daga dukan laifofina; kada ka sa in zama abin dariya ga wawaye.
Délivre-moi de toutes mes transgressions. Ne faites pas de moi l'objet de reproches de la part des fous.
9 Na yi shiru; ba zan buɗe bakina ba, gama kai ne wanda ka aikata wannan.
J'étais muet. Je n'ai pas ouvert la bouche, parce que tu l'as fait.
10 Ka ɗauke bulalarka daga gare ni; na ji jiki ta wurin bugun da hannunka ya yi mini.
Retire ton fléau loin de moi. Je suis vaincu par le coup de ta main.
11 Kakan tsawata ka kuma hore mutane saboda zunubinsu; kakan cinye wadatarsu kamar yadda asu ke yi, kowane mutum dai shaƙar iska ne. (Sela)
Quand tu réprimandes et corriges un homme pour une iniquité, vous consommez sa richesse comme un papillon de nuit. Certes, chaque homme n'est qu'un souffle. (Selah)
12 “Ka ji addu’ata, ya Ubangiji, ka saurari kukata ta neman taimako; kada ka kurmance ga kukata. Gama ina zama tare da kai kamar baƙo, baƙo, kamar yadda dukan kakannina sun kasance.
« Écoute ma prière, Yahvé, et prête l'oreille à mon cri. Ne restez pas silencieux devant mes larmes. Car je suis un étranger parmi vous, un étranger, comme l'étaient tous mes pères.
13 Ka kau da fuskarka daga gare ni, saboda in sāke yin farin ciki kafin in tafi in kuma rabu da nan.”
Oh, épargnez-moi, que je reprenne des forces, avant que je ne parte et que je n'existe plus. »