< Zabura 39 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zabura ta Dawuda. Na ce, “Zan lura da hanyoyina zan kuma kiyaye harshena daga zunubi; zan sa linzami a bakina muddin mugaye suna a gabana.”
To the choirmaster (for Jeduthun *Q(K)*) a psalm of David. I said I will guard ways my from sinning with tongue my I will keep to mouth my a muzzle while still [the] wicked [is] to before me.
2 Na yi shiru, ban ce kome ba, Ko a kan abin da yake da kyau! Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi;
I was dumb silence I was silent from good and pain my it was stirred up.
3 zuciyata ta ƙara zafi a cikina. Kuma sa’ad da nake tunani, wuta ta yi ta kuna; sai na yi magana da harshena na ce,
It became hot heart my - in inner being my in sighing my it burned fire I spoke with tongue my.
4 “Nuna mini, ya Ubangiji, ƙarshen rayuwata da kuma yawan kwanakina; bari in san yadda rayuwata tana wucewa da sauri.
Make known to me O Yahweh - end my and [the] measure of days my what? [is] it let me know how! fleeting [am] I.
5 Ka sa kwanakina suka zama tafin hannu ne kawai; yawan shekaruna kamar ba kome ba ne a gabanka. Duk ran mutum shaƙar iska ne kurum, har ma waɗanda suke tsammani suke da kāriya. (Sela)
Here! handbreadths - you have made days my and lifespan my [is] like nothing before you [is] only all vanity all humankind [which] stands (Selah)
6 “Mutum dai shirim ne kawai yayinda yake kai da komowa. Yana ta yawo, amma a banza ne kawai; yakan tara dukiya, ba tare da sanin wa zai more ta ba.
Only an image - he goes about a person only vanity people are in turmoil! he heaps up and not he knows who? [will be] gathering them.
7 “Amma yanzu, ya Ubangiji, me zan nema? Begena yana a gare ka.
And now what? do I wait for O Lord hope my [is] to you it.
8 Ka cece ni daga dukan laifofina; kada ka sa in zama abin dariya ga wawaye.
From all transgressions my deliver me a reproach of [the] foolish may not you make me.
9 Na yi shiru; ba zan buɗe bakina ba, gama kai ne wanda ka aikata wannan.
I am dumb not I open mouth my for you you have acted.
10 Ka ɗauke bulalarka daga gare ni; na ji jiki ta wurin bugun da hannunka ya yi mini.
Remove from on me plague your from [the] hostility of hand your I I have come to an end.
11 Kakan tsawata ka kuma hore mutane saboda zunubinsu; kakan cinye wadatarsu kamar yadda asu ke yi, kowane mutum dai shaƙar iska ne. (Sela)
With rebukes on iniquity - you have disciplined a person and you have melted like moth desired [thing] his [is] only vanity all humankind (Selah)
12 “Ka ji addu’ata, ya Ubangiji, ka saurari kukata ta neman taimako; kada ka kurmance ga kukata. Gama ina zama tare da kai kamar baƙo, baƙo, kamar yadda dukan kakannina sun kasance.
Hear! prayer my - O Yahweh and cry for help my - give ear to! to tear[s] my may not you be silent for [am] a sojourner I with you a resident alien like all ancestors my.
13 Ka kau da fuskarka daga gare ni, saboda in sāke yin farin ciki kafin in tafi in kuma rabu da nan.”
Smear from me so let me be cheerful before I will go and there not [will be] me.