< Zabura 39 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zabura ta Dawuda. Na ce, “Zan lura da hanyoyina zan kuma kiyaye harshena daga zunubi; zan sa linzami a bakina muddin mugaye suna a gabana.”
“A psalm of David. For the leader of the music of the Jeduthunites.” I said, I will take heed to my ways, That I may not sin with my tongue; I will keep my mouth with a bridle, While the wicked is before me.
2 Na yi shiru, ban ce kome ba, Ko a kan abin da yake da kyau! Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi;
I was dumb with silence; I spake not even what was good; But my pain was increased.
3 zuciyata ta ƙara zafi a cikina. Kuma sa’ad da nake tunani, wuta ta yi ta kuna; sai na yi magana da harshena na ce,
My heart was hot within me; In my anguish the fire burst forth, And I spake with my tongue:
4 “Nuna mini, ya Ubangiji, ƙarshen rayuwata da kuma yawan kwanakina; bari in san yadda rayuwata tana wucewa da sauri.
LORD, make me to know mine end, And the number of my days, That I may know how frail I am!
5 Ka sa kwanakina suka zama tafin hannu ne kawai; yawan shekaruna kamar ba kome ba ne a gabanka. Duk ran mutum shaƙar iska ne kurum, har ma waɗanda suke tsammani suke da kāriya. (Sela)
Behold, thou hast made my days as a hand-breadth, And my life is as nothing before thee; Yea, every man in his firmest state is altogether vanity. (Pause)
6 “Mutum dai shirim ne kawai yayinda yake kai da komowa. Yana ta yawo, amma a banza ne kawai; yakan tara dukiya, ba tare da sanin wa zai more ta ba.
Surely every man walketh in a vain show; Surely he disquieteth himself in vain; He heapeth up riches, and knoweth not who shall gather them.
7 “Amma yanzu, ya Ubangiji, me zan nema? Begena yana a gare ka.
What, then, O Lord! is my hope? My hope is in thee!
8 Ka cece ni daga dukan laifofina; kada ka sa in zama abin dariya ga wawaye.
Deliver me from all my transgressions; Let me not be the reproach of scoffers!
9 Na yi shiru; ba zan buɗe bakina ba, gama kai ne wanda ka aikata wannan.
Yet I am dumb; I open not my mouth; For thou hast done it!
10 Ka ɗauke bulalarka daga gare ni; na ji jiki ta wurin bugun da hannunka ya yi mini.
But remove from me thine infliction; For I am perishing by the blow of thine hand.
11 Kakan tsawata ka kuma hore mutane saboda zunubinsu; kakan cinye wadatarsu kamar yadda asu ke yi, kowane mutum dai shaƙar iska ne. (Sela)
When thou with rebukes dost chasten man for iniquity, Thou causest his glory to waste away like a moth! Surely every man is vanity.
12 “Ka ji addu’ata, ya Ubangiji, ka saurari kukata ta neman taimako; kada ka kurmance ga kukata. Gama ina zama tare da kai kamar baƙo, baƙo, kamar yadda dukan kakannina sun kasance.
Hear my prayer, O LORD! Give ear to my cry; Be not silent at my tears! For I am but a stranger with thee, A sojourner, as all my fathers were.
13 Ka kau da fuskarka daga gare ni, saboda in sāke yin farin ciki kafin in tafi in kuma rabu da nan.”
O spare me, that I may recover strength, Before I go away, and be no more!

< Zabura 39 >