< Zabura 39 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zabura ta Dawuda. Na ce, “Zan lura da hanyoyina zan kuma kiyaye harshena daga zunubi; zan sa linzami a bakina muddin mugaye suna a gabana.”
Kuom jatend wer. Ne Jeduthun. Zaburi mar Daudi. Ne awacho niya, “Abiro ritora e yorena, kendo abiro rito lewa kik wach richo; abiro tweyo dhoga gi tol kinde duto ma joma timbegi richo ni buta.”
2 Na yi shiru, ban ce kome ba, Ko a kan abin da yake da kyau! Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi;
To e seche mane ok awuo kendo alingʼ mos, kane ok awach gimoro amora maber, pek manie chunya nomedore.
3 zuciyata ta ƙara zafi a cikina. Kuma sa’ad da nake tunani, wuta ta yi ta kuna; sai na yi magana da harshena na ce,
Chunya nodoko maliet e iya kendo kane amedo paro matut, to nomedo bedo malit; eka ne atingʼo dhoga mi awuoyo:
4 “Nuna mini, ya Ubangiji, ƙarshen rayuwata da kuma yawan kwanakina; bari in san yadda rayuwata tana wucewa da sauri.
Yaye Jehova Nyasaye, nyisa giko mar ngimana bende nyisa kar romb ndalona; mondo abed ka angʼeyo ni ndalona kadho piyo.
5 Ka sa kwanakina suka zama tafin hannu ne kawai; yawan shekaruna kamar ba kome ba ne a gabanka. Duk ran mutum shaƙar iska ne kurum, har ma waɗanda suke tsammani suke da kāriya. (Sela)
Iseketo ndalona obedo machiek ka bad dhano; kar romb higni maga ok gimoro e nyimi, ngima dhano ka dhano en mana muya nono. (Sela)
6 “Mutum dai shirim ne kawai yayinda yake kai da komowa. Yana ta yawo, amma a banza ne kawai; yakan tara dukiya, ba tare da sanin wa zai more ta ba.
Dhano en mana tipo makadho kata ka owuotho koni gi koni, orikni gi tijene mapile kayiem; ochoko mwandu mathoth ka ok ongʼeyo ngʼama obiro weyonegi.
7 “Amma yanzu, ya Ubangiji, me zan nema? Begena yana a gare ka.
To koro, yaye Ruoth, en angʼo ma amanyo? Genona aketo kuomi.
8 Ka cece ni daga dukan laifofina; kada ka sa in zama abin dariya ga wawaye.
Resa kuom ketho maga duto; kik imi abedi ngʼama joma ofuwo jaro.
9 Na yi shiru; ba zan buɗe bakina ba, gama kai ne wanda ka aikata wannan.
Ne alingʼ alingʼa, kendo ne ok anyal yawo dhoga mondo awuo, nikech in ema isetimo ma.
10 Ka ɗauke bulalarka daga gare ni; na ji jiki ta wurin bugun da hannunka ya yi mini.
Gol chwat ma isechwadago oko; goch ma lweti goyago ohinga.
11 Kakan tsawata ka kuma hore mutane saboda zunubinsu; kakan cinye wadatarsu kamar yadda asu ke yi, kowane mutum dai shaƙar iska ne. (Sela)
Ikwero ji kikumogi nikech richogi; itieko mwandugi mana kaka thuth tieko oduma, dhano ka dhano en mana muya nono. (Sela)
12 “Ka ji addu’ata, ya Ubangiji, ka saurari kukata ta neman taimako; kada ka kurmance ga kukata. Gama ina zama tare da kai kamar baƙo, baƙo, kamar yadda dukan kakannina sun kasance.
Winj lamona, yaye Jehova Nyasaye, chik iti ni lamona ma adwarogo kony; kik idin iti ne ywakna, nikech adak kodi mana ka japiny moro, an mana wendo kaka kwerena duto ne gin.
13 Ka kau da fuskarka daga gare ni, saboda in sāke yin farin ciki kafin in tafi in kuma rabu da nan.”
We ngʼiya, mondo achak abed moil kendo kapok adar aweyo pinyni mi alal e wangʼ ji.