< Zabura 39 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zabura ta Dawuda. Na ce, “Zan lura da hanyoyina zan kuma kiyaye harshena daga zunubi; zan sa linzami a bakina muddin mugaye suna a gabana.”
Til Sangmesteren. Til Jedutun. En Salme af David.
2 Na yi shiru, ban ce kome ba, Ko a kan abin da yake da kyau! Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi;
Jeg sagde: »Mine Veje vil jeg vogte paa, saa jeg ikke synder med Tungen; min Mund vil jeg holde i Tømme, saa længe den gudløse er mig nær!«
3 zuciyata ta ƙara zafi a cikina. Kuma sa’ad da nake tunani, wuta ta yi ta kuna; sai na yi magana da harshena na ce,
Jeg var stum og tavs, jeg tav for at undgaa tomme Ord, men min Smerte naged,
4 “Nuna mini, ya Ubangiji, ƙarshen rayuwata da kuma yawan kwanakina; bari in san yadda rayuwata tana wucewa da sauri.
mit Hjerte brændte i Brystet, Ild lued op, mens jeg grunded; da talte jeg med min Tunge.
5 Ka sa kwanakina suka zama tafin hannu ne kawai; yawan shekaruna kamar ba kome ba ne a gabanka. Duk ran mutum shaƙar iska ne kurum, har ma waɗanda suke tsammani suke da kāriya. (Sela)
Lær mig, HERRE, at kende mit Endeligt, det Maal af Dage, jeg har, lad mig kende, hvor snart jeg skal bort!
6 “Mutum dai shirim ne kawai yayinda yake kai da komowa. Yana ta yawo, amma a banza ne kawai; yakan tara dukiya, ba tare da sanin wa zai more ta ba.
Se, i Haandsbredder maalte du mine Dage ud, mit Liv er som intet for dig, som et Aandepust staar hvert Menneske der. (Sela)
7 “Amma yanzu, ya Ubangiji, me zan nema? Begena yana a gare ka.
Kun som en Skygge er Menneskets Vandring, kun Tomhed er deres Travlhed; de samler og ved ej, hvem der faar det.
8 Ka cece ni daga dukan laifofina; kada ka sa in zama abin dariya ga wawaye.
Hvad bier jeg, Herre, da efter? Mit Haab staar ene til dig.
9 Na yi shiru; ba zan buɗe bakina ba, gama kai ne wanda ka aikata wannan.
Fri mig for al min Synd, gør mig ikke til Spot for Daarer!
10 Ka ɗauke bulalarka daga gare ni; na ji jiki ta wurin bugun da hannunka ya yi mini.
Jeg tier og aabner ikke min Mund, du voldte det jo.
11 Kakan tsawata ka kuma hore mutane saboda zunubinsu; kakan cinye wadatarsu kamar yadda asu ke yi, kowane mutum dai shaƙar iska ne. (Sela)
Borttag din Plage fra mig, under din vældige Haand gaar jeg til.
12 “Ka ji addu’ata, ya Ubangiji, ka saurari kukata ta neman taimako; kada ka kurmance ga kukata. Gama ina zama tare da kai kamar baƙo, baƙo, kamar yadda dukan kakannina sun kasance.
Naar du tugter en Mand med Straf for hans Brøde, smuldrer du hans Herlighed hen som Møl; kun et Aandepust er hvert Menneske. (Sela)
13 Ka kau da fuskarka daga gare ni, saboda in sāke yin farin ciki kafin in tafi in kuma rabu da nan.”
Hør, o HERRE, min Bøn og lyt til mit Skrig, til mine Taarer tie du ej! Thi en fremmed er jeg hos dig, en Gæst som alle mine Fædre. Se bort fra mig, saa jeg kvæges, før jeg gaar bort og ej mer er til!

< Zabura 39 >