< Zabura 39 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zabura ta Dawuda. Na ce, “Zan lura da hanyoyina zan kuma kiyaye harshena daga zunubi; zan sa linzami a bakina muddin mugaye suna a gabana.”
За първия певец Едутун. Давидов псалом. Рекох: Ще внимавам в пътищата си За да не съгреша с езика си. Ще имам юзда за устата си. Докато е пред мене нечестивият.
2 Na yi shiru, ban ce kome ba, Ko a kan abin da yake da kyau! Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi;
Станах ням и мълчалив, Въздържах се от да говоря, и нямах спокойствие; И скръбта ми се раздвижваше.
3 zuciyata ta ƙara zafi a cikina. Kuma sa’ad da nake tunani, wuta ta yi ta kuna; sai na yi magana da harshena na ce,
Сгорещи се сърцето ми дълбоко в мене; Докато размишлявах пламна огън. Тогава проговорих с езика си, казвайки:
4 “Nuna mini, ya Ubangiji, ƙarshen rayuwata da kuma yawan kwanakina; bari in san yadda rayuwata tana wucewa da sauri.
Научи ме, Господи, за кончината ми, И за числото на дните ми, какво е; Дай ми да зная колко съм кратковременен.
5 Ka sa kwanakina suka zama tafin hannu ne kawai; yawan shekaruna kamar ba kome ba ne a gabanka. Duk ran mutum shaƙar iska ne kurum, har ma waɗanda suke tsammani suke da kāriya. (Sela)
Ето направили си дните като педя. И възрастта ми е като нищо пред Тебе;
6 “Mutum dai shirim ne kawai yayinda yake kai da komowa. Yana ta yawo, amma a banza ne kawai; yakan tara dukiya, ba tare da sanin wa zai more ta ba.
Наистина всеки човек, колкото и яко да стои е само лъх, (Села) Наистина всеки човек ходи като сянка; Наистина всяка нищожност го смущава; Трупа съкровища, но не знае кой ще ги придобие.
7 “Amma yanzu, ya Ubangiji, me zan nema? Begena yana a gare ka.
И сега, Господи, що чакам? Надеждата ми е на Тебе.
8 Ka cece ni daga dukan laifofina; kada ka sa in zama abin dariya ga wawaye.
Избави ме от всичките ми беззакония.
9 Na yi shiru; ba zan buɗe bakina ba, gama kai ne wanda ka aikata wannan.
Онемях, не си отворих устата; Понеже Ти стори това.
10 Ka ɗauke bulalarka daga gare ni; na ji jiki ta wurin bugun da hannunka ya yi mini.
Отдалечи от мене удара Си; От поражението на ръката Ти изчезвам.
11 Kakan tsawata ka kuma hore mutane saboda zunubinsu; kakan cinye wadatarsu kamar yadda asu ke yi, kowane mutum dai shaƙar iska ne. (Sela)
Когато с изобличения наказваш човека за беззаконието му, Ти разваляш като молец красотата му. Наистина всеки човек е само лъх; (Села)
12 “Ka ji addu’ata, ya Ubangiji, ka saurari kukata ta neman taimako; kada ka kurmance ga kukata. Gama ina zama tare da kai kamar baƙo, baƙo, kamar yadda dukan kakannina sun kasance.
Послушай, Господи, молитвата ми, и дай ухо на вика ми; Не премълчавай при сълзите ми, Защото съм странен при Тебе И пришълец, както всичките мои бащи.
13 Ka kau da fuskarka daga gare ni, saboda in sāke yin farin ciki kafin in tafi in kuma rabu da nan.”
Остави ме да отдъхна, за да се съвзема Преди да си отида и да ме няма вече.