< Zabura 38 >

1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Dawid dwom. Adesrɛ. Awurade, nka mʼanim wɔ wʼabufuw mu na ntwe mʼaso wɔ wʼabufuwhyew mu.
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
Wo bɛmma hwirew me mu, na wo nsa adwerɛw me.
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
Wʼabufuwhyew no nti ahoɔden biara nni me mu; me bɔne nti, me nnompe ahodwow.
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
Mʼafɔdi amene me te sɛ adesoa a mu yɛ duru dodo.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
Mʼakuru bɔn na aporɔw esiane me bɔne mu agyimisɛm nti.
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
Makotow na wɔabrɛ me ase; da mu nyinaa menantenantew twa agyaadwo.
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
Mʼakyi dompe mu yaw boro so: ahoɔden biara nni me nipadua mu.
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
Mabrɛ na mapɛtɛw koraa. Me koma mu yaw ma misi apini.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
Awurade, nea merehwɛ anim nyinaa da wʼanim; mʼapinisi nhintaw wo.
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
Me koma bɔ kitirikitiri, na mʼahoɔden asa mpo mʼaniwa aduru sum.
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
Mʼapirakuru nti me nnamfonom ne me yɔnkonom mmɛn me; mʼafipamfo twe wɔn ho fi me ho.
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
Wɔn a wɔpɛ sɛ wokum me no sum me mfiri, wɔn a wɔpɛ sɛ wɔhaw me no di me sɛe ho nkɔmmɔ da mu nyinaa wodwen nnaadaasɛm ho.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
Mete sɛ ɔsotifo a ɔnte asɛm, mete sɛ mum a ontumi nkasa.
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
Mayɛ sɛ obi a ɔnte asɛm, nea nʼano ntumi mma mmuae.
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
Awurade, meretwɛn wo; Awurade me Nyankopɔn, wubegye me so.
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
Mekae se, “Mma wɔn ani nnye; anaa wɔmma wɔn ho so bere a mʼanan awatiri no.”
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
Mereyɛ mahwe ase, na me yaw da so wɔ me mu.
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
Meka me mfomso kyerɛ; me bɔne hyɛ me so.
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
Bebree na wɔyɛ mʼatamfo; wɔn a wɔtan me kwa no dɔɔso.
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
Wɔn a wɔde bɔne tua me papa so ka no, bɔ me ahohora bere a mereyɛ papa.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
Awurade nnyaw me. Me Nyankopɔn, nkɔ akyiri!
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
Bra ntɛm bɛboa me, Awurade, mʼAgyenkwa. Wɔde ma dwonkyerɛfo no. Yedutun.

< Zabura 38 >