< Zabura 38 >

1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Salmo de David, para recordar. JEHOVÁ, no me reprendas en tu furor, ni me castigues en tu ira.
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
Porque tus saetas descendieron á mí, y sobre mí ha caído tu mano.
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
No hay sanidad en mi carne á causa de tu ira; ni hay paz en mis huesos á causa de mi pecado.
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
Porque mis iniquidades han pasado mi cabeza: como carga pesada se han agravado sobre mí.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
Pudriéronse, corrompiéronse mis llagas, á causa de mi locura.
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
Estoy encorvado, estoy humillado en gran manera, ando enlutado todo el día.
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
Porque mis lomos están llenos de irritación, y no hay sanidad en mi carne.
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
Estoy debilitado y molido en gran manera; bramo á causa de la conmoción de mi corazón.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
Señor, delante de ti están todos mis deseos; y mi suspiro no te es oculto.
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
Mi corazón está acongojado, hame dejado mi vigor; y aun la misma luz de mis ojos no está conmigo.
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
Mis amigos y mis compañeros se quitaron de delante de mi plaga; y mis cercanos se pusieron lejos.
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
Y los que buscaban mi alma armaron lazos; y los que procuraban mi mal hablaban iniquidades, y meditaban fraudes todo el día.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
Mas yo, como [si fuera] sordo, no oía; [y estaba] como un mudo, [que] no abre su boca.
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
Fuí pues como un hombre que no oye, y que en su boca no tiene reprensiones.
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
Porque á ti, oh Jehová, esperé yo: tú responderás, Jehová Dios mío.
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
Porque dije: Que no se alegren de mí: cuando mi pie resbalaba, sobre mí se engrandecían.
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
Empero yo estoy á pique de claudicar, y mi dolor está delante de mí continuamente.
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
Por tanto denunciaré mi maldad; congojaréme por mi pecado.
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
Porque mis enemigos están vivos [y] fuertes: y hanse aumentado los que me aborrecen sin causa:
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
Y pagando mal por bien me son contrarios, por seguir yo lo bueno.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
No me desampares, oh Jehová: Dios mío, no te alejes de mí.
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
Apresúrate á ayudarme, oh Señor, mi salud.

< Zabura 38 >