< Zabura 38 >

1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Psalm Davidov za spomin. Gospod, v srdu svojem ne dólži me, in v togoti svoji ne pokôri me.
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
Ker pušice tvoje so zasajene v mé, in nadme si spustil roko svojo.
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
Nič celega ni na mesu mojem zavoljo srdú tvojega; mirú ni v mojih kostéh zavoljo greha mojega.
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
Ker krivice moje presezajo glavo mojo, kakor težko breme; pretežke so, da bi jih prenašati mogel.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
Segnjile so in usmradile se bule moje, zavoljo nespameti moje.
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
Mučim se, krivim se presilno, ves dan pohajam v črni obleki.
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
Ker drob moj je poln prisada, tako da ni nič celega na mesu mojem.
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
Oslabljen sem in potrt presilno; tulim od stokanja svojega srca.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
Gospod, pred teboj je vse hrepenenje moje; in zdihovanje ni ti skrito.
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
Srce moje utriplje, zapušča me moja krepost, in luč mojih očî, tudi one niso v moji oblasti.
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
Prijátelji moji in bližnji moji stojé nadlogi moji nasproti, in sorodniki moji stojé od daleč.
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
Stavijo pa zanke, kateri iščejo duše moje: in kateri iščejo hudega meni, govoré nadloge in izmišljajo ves dan zvijače.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
Jaz pa jih ne slišim kakor gluh, in kakor nem ne odprem svojih ust.
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
Ampak sem kakor ón, ki ne sliši, in kateremu ní dokazov v ustih.
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
Ker tebe čakam, Gospod; da me ti uslišiš, Gospod, Bog moj.
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
Ker pravim: Naj se ne radujejo nad menoj; ko omahuje noga moja, naj se ne povzdigujejo proti meni,
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
Ako bodem jaz za omahnenje pripravljen, in bolečina moja bode vedno pred mano.
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
Ker krivico svojo oznanjam, skrbi me moj greh.
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
Neprijatelji pa moji krepčajo se živi, in množijo se, kateri me sovražijo iz krivih vzrokov.
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
In vračajoč hudo za dobro nasprotujejo mi, zato ker hodim za dobrim.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
Ne zapústi me, Gospod, Bog moj; ne bivaj daleč od mene.
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
Hiti na pomoč mojo, Gospod, blaginja moja!

< Zabura 38 >