< Zabura 38 >
1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Oh Gospod, ne oštevaj me v svojem besu niti me ne karaj v svojem silnem nezadovoljstvu.
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
Kajti tvoje puščice trdno tičijo v meni in tvoja roka me boleče pritiska.
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
Zaradi tvoje jeze na mojem mesu ni zdravja niti ni v mojih kosteh zaradi mojega greha nobenega počitka.
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
Kajti moje krivičnosti so presegle mojo glavo, kakor težko breme so zame pretežke.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
Moje rane zaudarjajo in so okužene zaradi moje nespametnosti.
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
Zaskrbljen sem, silno sem sklonjen, ves dan hodim in žalujem.
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
Kajti moja ledja so napolnjena z gnusno boleznijo in zdravja ni na mojem mesu.
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
Slaboten sem in boleče zlomljen, vpil sem zaradi nemira v svojem srcu.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
Gospod, pred teboj je vse moje hrepenenje in moje stokanje ni skrito pred teboj.
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
Moje srce trepeta, moja moč me zapušča. Glede svetlobe mojih oči, je tudi ta odšla od mene.
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
Moji ljubi in moji prijatelji stojijo daleč stran od moje rane in moji sorodniki stojijo daleč stran.
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
Tudi tisti, ki mi strežejo po življenju, zame postavljajo zanke in tisti, ki iščejo mojo bolečino, govorijo pogubne stvari in si ves dan domišljajo prevare.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
Toda jaz, kakor gluh človek, nisem slišal in bil sem nem človek, ki ne odpira svojih ust.
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
Tako sem bil človek, ki ne sliši in v čigar ustih ni opominov.
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
Kajti vate zaupam, oh Gospod, ti boš uslišal, oh Gospod, moj Bog.
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
Kajti rekel sem: » Usliši me, da se ne bi sicer veselili nad menoj. Ko moje stopalo zdrsuje, se poveličujejo proti meni.«
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
Kajti pripravljen sem, da se zaustavim in moja bridkost je nenehno pred menoj.
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
Kajti oznanil bom svojo krivičnost, žalosten bom zaradi svojega greha.
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
Toda moji sovražniki so živi in oni so močni, in tisti, ki me krivično sovražijo, so pomnoženi.
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
Tudi tisti, ki vračajo zlo za dobro, so moji nasprotniki, ker sledim stvari, ki je dobra.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
Ne zapusti me, oh Gospod. Oh moj Bog, ne bodi daleč od mene.
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
Podvizaj se, da mi pomagaš, oh Gospod, rešitev moje duše.