< Zabura 38 >
1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
psalmus David in rememorationem de sabbato Domine ne in furore tuo arguas me neque in ira tua corripias me
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
quoniam sagittae tuae infixae sunt mihi et confirmasti super me manum tuam
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
non est sanitas carni meae a facie irae tuae non est pax ossibus meis a facie peccatorum meorum
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
quoniam iniquitates meae supergressae sunt caput meum sicut onus grave gravatae sunt super me
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
putruerunt et corruptae sunt cicatrices meae a facie insipientiae meae
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
miser factus sum et curvatus sum usque ad finem tota die contristatus ingrediebar
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
quoniam lumbi mei impleti sunt inlusionibus et non est sanitas in carne mea
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
adflictus sum et humiliatus sum nimis rugiebam a gemitu cordis mei
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
Domine ante te omne desiderium meum et gemitus meus a te non est absconditus
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
cor meum conturbatum est dereliquit me virtus mea et lumen oculorum meorum et ipsum non est mecum
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
amici mei et proximi mei adversus me adpropinquaverunt et steterunt et qui iuxta me erant de longe steterunt
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
et vim faciebant qui quaerebant animam meam et qui inquirebant mala mihi locuti sunt vanitates et dolos tota die meditabantur
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
ego autem tamquam surdus non audiebam et sicut mutus non aperiens os suum
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
et factus sum sicut homo non audiens et non habens in ore suo redargutiones
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
quoniam in te Domine speravi tu exaudies Domine Deus meus
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
quia dixi nequando supergaudeant mihi inimici mei et dum commoventur pedes mei super me magna locuti sunt
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
quoniam ego in flagella paratus et dolor meus in conspectu meo semper
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
quoniam iniquitatem meam adnuntiabo et cogitabo pro peccato meo
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
inimici autem mei vivent et firmati sunt super me et multiplicati sunt qui oderunt me inique
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
qui retribuunt mala pro bonis detrahebant mihi quoniam sequebar bonitatem
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
non derelinquas me Domine Deus meus ne discesseris a me
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
intende in adiutorium meum Domine salutis meae