< Zabura 38 >
1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Salmo. Di Davide. In memoria. Signore, non castigarmi nel tuo sdegno, non punirmi nella tua ira.
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
Le tue frecce mi hanno trafitto, su di me è scesa la tua mano.
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
Per il tuo sdegno non c'è in me nulla di sano, nulla è intatto nelle mie ossa per i miei peccati.
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
Le mie iniquità hanno superato il mio capo, come carico pesante mi hanno oppresso.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
Putride e fetide sono le mie piaghe a causa della mia stoltezza.
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
Sono curvo e accasciato, triste mi aggiro tutto il giorno.
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
Sono torturati i miei fianchi, in me non c'è nulla di sano.
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
Afflitto e sfinito all'estremo, ruggisco per il fremito del mio cuore.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
Signore, davanti a te ogni mio desiderio e il mio gemito a te non è nascosto.
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
Palpita il mio cuore, la forza mi abbandona, si spegne la luce dei miei occhi.
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
Amici e compagni si scostano dalle mie piaghe, i miei vicini stanno a distanza.
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
Tende lacci chi attenta alla mia vita, trama insidie chi cerca la mia rovina. e tutto il giorno medita inganni.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
Io, come un sordo, non ascolto e come un muto non apro la bocca;
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
sono come un uomo che non sente e non risponde.
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
In te spero, Signore; tu mi risponderai, Signore Dio mio.
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
Ho detto: «Di me non godano, contro di me non si vantino quando il mio piede vacilla».
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
Poiché io sto per cadere e ho sempre dinanzi la mia pena.
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
Ecco, confesso la mia colpa, sono in ansia per il mio peccato.
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
I miei nemici sono vivi e forti, troppi mi odiano senza motivo,
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
mi pagano il bene col male, mi accusano perché cerco il bene.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
Non abbandonarmi, Signore, Dio mio, da me non stare lontano;
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
accorri in mio aiuto, Signore, mia salvezza.