< Zabura 38 >

1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Ein Psalm von David, bei Darbringung des Duftopfers. HERR, nicht in deinem Zorne strafe mich,
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
Denn deine Pfeile sind in mich eingedrungen, und deine Hand liegt schwer auf mir:
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
nichts ist gesund an meinem Leib ob deinem Zürnen, nichts heil an meinen Gliedern ob meiner Sünde.
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
Denn meine Missetaten schlagen mir über dem Haupt zusammen; wie eine schwere Last sind sie mir zu schwer geworden.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
Es faulen, es eitern meine Wunden infolge meiner Torheit.
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
Ich bin gekrümmt, tief niedergebeugt; den ganzen Tag geh’ ich trauernd einher;
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
denn meine Lenden sind voll von Entzündung, und nichts ist unversehrt an meinem Leibe.
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
Erschöpft bin ich und ganz zerschlagen, ich schreie auf infolge des Stöhnens meines Herzens.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
O Allherr, all mein Verlangen ist dir bekannt, und meine Seufzer sind dir nicht verborgen.
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
Mein Herz pocht stürmisch, meine Kraft hat mich verlassen, und das Licht meiner Augen, auch das ist dahin!
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
Meine Freunde und Genossen stehn abseits von meinem Elend, und meine nächsten Verwandten halten sich fern.
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
Die nach dem Leben mir trachten, legen mir Schlingen, und die mein Unglück suchen, verabreden Unheil und sinnen auf Trug den ganzen Tag.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
Doch ich bin wie ein Tauber, höre es nicht, und bin wie ein Stummer, der den Mund nicht auftut;
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
ja, ich bin wie einer, der nicht hören kann und in dessen Mund keine Widerrede ist;
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
denn auf dich, HERR, warte ich: du wirst antworten, o Allherr, mein Gott;
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
denn ich sage: »Daß sie nur nicht über mich frohlocken, nur nicht beim Wanken meines Fußes gegen mich großtun!«
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
Denn nahe bin ich am Zusammenbrechen, und mein Schmerz ist mir allezeit gegenwärtig.
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
Ach! Ich bekenne meine Schuld, bin bekümmert ob meiner Sünde!
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
Dagegen die ohne Grund mich befeinden, sind stark, und zahlreich sind, die ohn’ Ursach’ mich hassen,
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
und solche, die mir Gutes mit Bösem vergelten, sind meine Widersacher, weil fest am Guten ich halte.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
Verlaß mich nicht, o HERR, mein Gott, sei nicht ferne von mir!
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
Eile zu meinem Schutz herbei, o Allherr, meine Rettung!

< Zabura 38 >