< Zabura 38 >
1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Ein Psalm von David zum Gedächtnis. Jehova, strafe mich nicht in deinem Zorn, noch züchtige mich in deinem Grimm!
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
Denn deine Pfeile sind in mich eingedrungen, und deine Hand hat sich auf mich herabgesenkt.
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
Nichts Heiles ist an meinem Fleische wegen deines Zürnens, kein Frieden in meinen Gebeinen wegen meiner Sünde.
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
Denn meine Ungerechtigkeiten sind über mein Haupt gegangen, wie eine schwere Last sind sie zu schwer für mich.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
Es stinken, es eitern meine Wunden wegen meiner Torheit.
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
Ich bin gekrümmt, über die Maßen gebeugt; den ganzen Tag gehe ich trauernd einher.
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
Denn voll Brand sind meine Lenden, und nichts Heiles ist an meinem Fleische.
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
Ich bin ermattet und über die Maßen zerschlagen, ich heule vor Gestöhn meines Herzens.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
Herr, vor dir ist all mein Begehr, und mein Seufzen ist nicht vor dir verborgen.
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
Mein Herz pocht, verlassen hat mich meine Kraft; und das Licht meiner Augen, auch das ist nicht bei mir.
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
Meine Lieben und meine Genossen stehen fernab von meiner Plage, und meine Verwandten stehen von ferne.
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
Und die nach meinem Leben trachten, legen mir Schlingen; und die mein Unglück suchen, reden von Schadentun und sinnen auf Trug den ganzen Tag.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
Ich aber, wie ein Tauber, höre nicht, und bin wie ein Stummer, der seinen Mund nicht auftut.
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
Und ich bin wie ein Mann, der nicht hört, und in dessen Munde keine Gegenreden sind.
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
Denn auf dich, Jehova, harre ich; du, du wirst antworten, Herr, mein Gott.
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
Denn ich sprach: Daß sie sich nicht über mich freuen! Beim Wanken meines Fußes tun sie groß wider mich.
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
Denn ich bin nahe daran zu hinken, und mein Schmerz ist beständig vor mir.
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
Denn ich tue kund meine Ungerechtigkeit; ich bin bekümmert wegen meiner Sünde.
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
Meine Feinde aber leben, sind stark, und viele sind derer, die ohne Grund mich hassen;
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
und Böses für Gutes vergeltend, feinden sie mich an, weil ich dem Guten nachjage.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
Verlaß mich nicht, Jehova; mein Gott, sei nicht fern von mir!
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
Eile zu meiner Hilfe, Herr, meine Rettung!