< Zabura 38 >

1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Éternel, ne me châtie pas dans ta colère, et ne me punis pas dans ton courroux!
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
Car tes flèches sont entrées en moi, et ta main s'est appesantie sur moi.
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
Il n'y a rien d'entier dans ma chair, à cause de ton courroux, ni aucun repos dans mes os, à cause de mon péché.
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
Car mes iniquités vont par-dessus ma tête; elles sont comme un lourd fardeau, trop pesant pour moi.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
Mes plaies sont fétides, et elles coulent, à cause de ma folie.
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
Je suis courbé, affaissé au dernier point; je marche en deuil tout le jour.
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
Car mes reins sont pleins d'inflammation; il n'y a rien d'entier dans ma chair.
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
Je suis affaibli et tout brisé; je rugis dans l'agitation de mon cœur.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
Seigneur, tout mon désir est devant toi, et mon gémissement ne t'est point caché.
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
Mon cœur palpite, ma force m'abandonne; et la lumière de mes yeux même, je ne l'ai plus.
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
Devant le coup qui me frappe, mes amis, mes compagnons s'arrêtent, et mes proches se tiennent loin.
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
Ceux qui en veulent à ma vie me tendent des pièges; ceux qui cherchent mon mal parlent de ruine, et chaque jour ils méditent des tromperies.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
Mais moi, comme un sourd, je n'entends point; je suis comme un muet qui n'ouvre point la bouche.
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
Oui, je suis comme un homme qui n'entend point, et qui n'a point de réplique en sa bouche.
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
Car c'est à toi, Éternel, que je m'attends; tu répondras, Seigneur, mon Dieu!
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
Car j'ai dit: Qu'ils ne se réjouissent pas à mon sujet! Quand mon pied glisse, ils s'élèvent contre moi.
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
Et je suis prêt à tomber, et ma douleur est toujours devant moi.
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
Car je déclare mon iniquité; je suis dans la crainte à cause de mon péché.
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
Cependant mes ennemis sont vivants et forts, et ceux qui me haïssent sans cause sont nombreux.
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
Et, me rendant le mal pour le bien, ils se font mes adversaires parce que je m'attache au bien.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
Ne m'abandonne point, ô Éternel! Mon Dieu, ne t'éloigne point de moi!
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
Hâte-toi, viens à mon aide, Seigneur, qui es ma délivrance!

< Zabura 38 >