< Zabura 38 >

1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Psaume de David, pour se souvenir du Sabbat. Seigneur, ne me réprimande pas dans ta fureur; ne me châtie pas dans ta colère.
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
Car tes flèches m'ont transpercé, et tu as appesanti sur moi ta main.
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
En ma chair il n'est plus rien de sain en face de ta colère; il n'est point de paix pour mes os en face de mes péchés.
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
Car mes iniquités se sont accumulées plus haut que ma tête; elles me pèsent comme un lourd fardeau.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
Mes meurtrissures sont infectes et gangrenées à cause de ma folie.
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
Je suis devenu misérable, entièrement courbé; j'ai marché tout le jour, plein de tristesse.
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
Mes flancs ont été remplis de moqueries, et il n'est rien de sain dans ma chair.
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
J'ai été affligé et j'ai été humilié à l'excès; je rugissais à cause des gémissements de mon cœur.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
Tout mon désir est devant toi; mon gémissement ne t'est point caché.
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
Mon cœur est troublé, ma force a défailli, et la lumière de mes yeux n'est point avec moi.
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
Mes amis et mes proches se sont avancés et arrêtés contre moi, et ceux qui m'approchaient de plus près se sont tenus au loin;
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
Tandis que j'étais pressé avec violence par ceux qui cherchaient à m'ôter la vie, et que ceux qui pensaient à mal contre moi disaient des paroles menteuses, et tout le long du jour inventaient des tromperies.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
Mais moi je ne les entendais non plus qu'un sourd, et comme un muet je n'ouvrais pas la bouche.
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
J'étais devenu semblable à un homme qui n'entend rien, et n'a rien à répliquer en sa bouche.
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
Car, ô Seigneur, j'espérais en toi, et tu m'exauceras, Seigneur mon Dieu!
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
Et j'ai dit: Que je ne sois point pour mes ennemis un sujet de joie, ceux qui parlaient orgueilleusement contre moi quand mes pieds étaient chancelants.
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
Car je suis prêt à être flagellé, et ma douleur m'est toujours présente.
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
Et je déclarerai mon iniquité; et je serai dans la douleur au sujet de mon péché.
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
Cependant mes ennemis sont vivants, et ils se sont fortifiés contre moi, et le nombre de ceux qui me haïssent injustement s'est multiplié.
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
Ceux qui rendent le mal pour le bien m'ont calomnié, parce que je recherchais la justice.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
Ne m'abandonne pas, Seigneur mon Dieu, ne te détourne point de moi.
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
Approche-toi pour me secourir, ô Dieu de mon salut!

< Zabura 38 >