< Zabura 38 >
1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Psaume de David, pour faire souvenir. Éternel! ne me reprends pas dans ta colère, et ne me châtie pas dans ta fureur.
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
Car tes flèches ont pénétré en moi, et ta main est descendue sur moi.
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
Il n’y a rien d’entier en ma chair, à cause de ton indignation; point de paix dans mes os, à cause de mon péché.
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
Car mes iniquités ont passé sur ma tête; comme un pesant fardeau, elles sont trop pesantes pour moi.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
Mes plaies sont fétides, elles coulent, à cause de ma folie.
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
Je suis accablé et extrêmement courbé; tout le jour je marche dans le deuil;
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
Car mes reins sont pleins d’inflammation, et il n’y a rien d’entier dans ma chair.
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
Je suis languissant et extrêmement brisé; je rugis dans le frémissement de mon cœur.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
Seigneur! tout mon désir est devant toi, et mon gémissement ne t’est point caché.
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
Mon cœur bat fort, ma force m’a abandonné, et la lumière de mes yeux aussi n’est plus avec moi.
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
Ceux qui m’aiment, et mes compagnons, se tiennent loin de ma plaie, et mes proches se tiennent à distance,
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
Et ceux qui cherchent ma vie me tendent des pièges, et ceux qui cherchent mon mal parlent de malheurs et disent des tromperies tout le jour.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
Et moi, comme un sourd, je n’entends pas, et, comme un muet, je n’ouvre pas la bouche.
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
Je suis devenu comme un homme qui n’entend point et dans la bouche duquel il n’y a pas de réplique.
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
Car je m’attends à toi, Éternel! Toi, tu répondras, Seigneur, mon Dieu!
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
Car j’ai dit: Qu’ils ne se réjouissent pas à mon sujet! Quand mon pied chancelle, ils s’élèvent orgueilleusement contre moi.
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
Car je suis prêt à boiter, et ma douleur est toujours devant moi;
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
Car je déclarerai mon iniquité; je suis en peine pour mon péché.
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
Et mes ennemis sont vivants, ils sont forts, et ceux qui me haïssent sans motif sont nombreux;
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
Et ceux qui me rendent le mal pour le bien sont mes adversaires, parce que je poursuis ce qui est bon.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
Éternel! ne m’abandonne point; mon Dieu! ne t’éloigne pas de moi.
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
Hâte-toi de me secourir, Seigneur, mon salut!